Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar a yau Juma’a cewa, daga ranar 9 zuwa 12 ga wata, wakilin musamman na shugaba Xi Jinping, Zhang Guoqing zai tafi kasar Faransa domin halartar taron koli kan ayyukan fasahar kirkirarriyar basira ta AI, bisa gayyatar da mai karbar bakuncin taron ta yi masa.

Zhang mamba ne na ofishin siyasa na kwamitin koli na jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin, kuma mai mukamin mataimakin firaminista a majalisar gudanarwar kasar Sin.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin, Lin Jian ya bayyana cewa, ta hanyar halartar taron, kasar Sin tana fatan karfafa cundayar juna da mu’amala da dukkan bangarori, da samar da daidaito kan hadin gwiwa, da kara matsa kaimi ga aiwatar da yarjejeniyar MDD kan fasahar zamani. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zhao Leji Ya Yi Jawabi A Babban Taron Shugabannin Majalisun Kasa Da Kasa Karo Na 6
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Shirya Taron Bita Ga Kansiloli
  • INEC Ta Gudanar da Taron Masu Ruwa da Tsaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi na Babura/Garki
  • Ministan Harkokin Wajen Siriya Yana Rasha Don Bude Sabon Shafi Tsakaninsu
  • Canada Zata Amince Da Samuwar Kasar Falasdinu A Taron MDD
  • An Yaba Da Kwazon Shugaba Bola Ahmad Tinubu
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata
  • Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana