Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dakta Ajuji Ahmed, ya tabbatar da shugabancinsa, inda ya yi watsi da ikirarin wani bangare na jam’iyyar, inda ya bayyana cewa shi ne wanda hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta amince da shi. Da yake magana a wani taron manema labarai a Abuja ranar Juma’a, Ahmed ya tabbatar da cewa, jam’iyyar na nan a karkashin shugabancinsa da kuma kwamitin ayyuka na kasa (NWC) da aka kaddamar a shekarar 2022.

Sin Ta Yi Watsi Da Tsegumin Da Marco Rubio Ya Yi Kan Hadin Gwiwarta Da Latin Amurka ‘Yansanda Sun Kama Mutum Uku Da Kokon Kan Mutum A Imo Dakta Ahmed ya jaddada cewa, INEC jam’iyyar NNPP daya ta sani, mai tambarin launin ja, fari, da jajayen kalamai, da littafi, da kuma hular ilimi mai taken, ilimi ga kowa, “Education for All”. Ya bukaci ‘yan Nijeriya da masu yada labarai da su tabbatar da ikirarinsa da ke shafin hukumar ta INEC. Da yake martani kan taron da wani bangare na jam’iyya NNPP ya gudanar a Legas kwanan nan, Dr. Ahmed ya yi watsi da taron, a matsayin taron da ya sabawa doka. Ya bayyana cewa, jam’iyyar bata gudanar da wani taro a wajen hedikwatarta da ke Abuja ba, ya kuma musanta ikirarin kaddamar da sabon kwamitin gudanarwa a wasu wurare sabanin na Abuja.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • INEC Ta Gudanar da Taron Masu Ruwa da Tsaki Kafin Zaɓen Cike Gurbi na Babura/Garki
  • Yanzu-yanzu: Sanata Dino Melaye Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Canada Zata Amince Da Samuwar Kasar Falasdinu A Taron MDD
  • 2027: Ba Mu Kafa Haɗakarmu Don Cika Burin Atiku Ba – ADC
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma