NCDC ta tsaurara matakan shige da fice a Nijeriya saboda fargabar Ebola
Published: 3rd, February 2025 GMT
Hukumar yaƙi da cututtuka masu yaɗuwa a Nijeriya (NCDC) ta tsaurara matakan sanya idanu akan hanyoyin shigowa ƙasar sakamakon sabuwar ɓarkewar cutar Ebola a Uganda.
NCDC ta gargaɗi ’yan ƙasar da su guji yin tafiye-tafiye zuwa Uganda saboda ɓullar cutar Ebola da aka tabbatar a ƙasar.
EU ta yaba wa Gwamna Zulum kan farfaɗo da Jihar Borno Masarautar Fika ta buɗe gasar ƙwallon ƙafa karo na uku a PotiskumShawarar NCDC na zuwa ne bayan sanarwar Ma’aikatar Lafiya ta Uganda a ranar 30 ga watan Janairun 2025 kan ɓarkewar wani nau’in cutar Ebola mai suna Sudan a gundumomin Wakiso da Mukono da kuma Mbale na ƙasar.
Ko da yake sanarwar NCDC ta ce ba a samu wani rahoto ba game da ɓullar cutar a Nijeriya, sai dai tun da fari dai Hukumar Lafiya ta Uganda ta ce cutar ta yi sanadiyar mutuwar wani mutum ɗaya kana ana kan bincike wasu 44 a ake zargin ya yi mu’amala da su kai-tsaye.
Sakamakon hakan, NCDC a cikin shawarwarin da ta fitar ta ce duk da cewar babu cutar a Nijeriya, amma tana aiki ne domin daƙile shigowarta.
“NCDC tana koƙari wajen sa ido a wuraren shige da fice a Nijeriya tare da sabunta tsare-tsaren bayar da agajin gaggawa da kuma hanyoyin bincike don gano cutar a manyan ɗakunan gwaje-gwaje da ake da su a manyan biranen da ke da filayen jiragen sama na ƙasa da ƙasa,” a cewar sanarwar gargaɗin da NCDC ta fitar wadda ke ɗauke da sa hannu Darakta Janar Jide Idris.
Haka kuma sanarwar ta ce “duk da cewa Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ba ta ayyana dokar hana tafiye-tafiye zuwa Uganda ba, ana gargaɗin duk wanda ya fito daga wuraren da aka samu ɓullar cutar a cikin kwanaki 21 da suka wuce, kuma yake nuna wasu alamomi kamar zazzaɓi da ciwon gabobi da makogwaro da amai da gudawa ko ciwon ciki da dai sauransu, ya gaggauta tuntuɓar Hukumar lafiya ta jihar da yake.”
Kazalika NCDC ta buƙaci ‘yan Nijeriya da su tabbatar an yi musu allurar riga-kafin wasu nau’in cutar Ebola duk kuwa da cewa a yanzu ƙasar ba ta da na nau’in cutar na Sudan da ya ɓarke a Uganda.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Iyakokin Nijeriya cutar Ebola
এছাড়াও পড়ুন:
Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara
A nasa jawabin, Gwamna Dauda Lawal ya yaba da ziyarar da cibiyar ta kai Zamfara domin duba ƙoƙarin gwamnati na magance matsalar rashin tsaro a jihar.
“Ina yawan cewa, idan ku ka yi ƙoƙarin shawo kan Zamfara yadda ya kamata ta fuskar rashin tsaro, za ku magance kashi 80 na matsalolin tsaro a Arewa.
“Daga dukkan tsare-tsaren da na gani ya zuwa yanzu, mun mallaki abin da ake buƙata domin tunkarar waɗannan ƙalubale bisa tuntubar juna da haxin gwiwa tsakanin jihar Zamfara da ofishin mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, wannan abin a yaba ne.
“Na yi farin ciki da jin cewa Tarayyar Turai ta ware wasu kuɗaɗe, duk da cewa za mu samar da wani asusu, a Zamfara a shirye muke mu ba da tallafin, idan kun shirya gobe, mu ma mun shirya.
“Mun shirya, kuma ƙofar mu a buɗe take, duk wani abu da zai kawo sauyi mai kyau a Zamfara muna maraba da shi, muna buƙatar tsari na abin da ku ke yi domin mu ci gaba da bin diddigin lamarin, zan samu wata tawaga da za ta riƙa hulɗa da cibiyar yaƙi da ta’addanci.
Tun da farko, Shugabar Rigakafi da Yaƙi da Ta’addanci (PCVE), Ambasada Mairo Musa Abbas ta ce, tawagar ta zo jihar Zamfara ne a madadin mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Mallam Nuhu Ribadu da kuma kodinetan yaƙi da ta’addanci na ƙasa, Manjo Janar Adamu Garba Laka. “Muna nan a matsayin wani bangare na dabarun bayar da shawarwari na ƙasa baki ɗaya.”
“Muna son sake gode muku bisa irin karramawar da ka yi mana a Jihar Zamfara da kuma irin shugabancin da ka yi wa al’umma, muna sa ran haɗin kai don ganin cewa Zamfara ta zama kan gaba wajen yaƙi da ‘yan bindiga.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp