Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka, Sharhin bayan labarammu zai yi magana a kan “jajircewar mutanen kudancin kasar Lebanon fuskantar sojojin HKI’ yan mamaya’ wanda ni tahir amin.

///…A Jiya lahadi be wa’adin ficewar HKI daga yankuna da garuruwan da suka mammaye a kudancin kasar Lebanon, amma karfe 4 da safe yana cika mutanen wadannan yankuna suka kwarara zuwa gidajensi, amma ko da suka isa sai suka ga cewa sojojin kasar Lebanon sun sha shinge don hana mutane wucewa zuwa wadannan wurare, don har yanzun akwai sojojin HKI a yankin suna iya kashe su.

Banda haka sojojin HKI sun kara wayoyin wasu daga cikin mutanen wadannan yankuna, suna fada masu cewa kada su kuskura su shiga wadannan yankuna.

Amma sai jerin gwanon mutoci da barbura da mutane masu takawa da kafa kake gani suna kwarara zuwa gidajensu. Gwamnatin kasar Amurka ta bukaci gwamnatin Lebanon su amince a kara lokacin janyewar sojojin HKI daga wadannan yankuna na kudancin kasar Lebanon, har zuwa 18 ga watan Fabrayru mai zuwa, amma gwamnatin ta ki amincea da hakan.

A jiya Lahadi sojojin HKI sun bude wuta kan wasu mutanen kudancin kasar Lebanon wadanda suke son komawa gidajensu, inda suka kashe mutane 18 suka kuma raunata wasu kimani 100 a yankunan daban daban da suke mamaye da su a kasar ta Lebanon.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya nakalto yadda al-amura suka tafiya a kudancin kasar Lebanon a safiyar ranar litinin, inda wasu suke cewa, ai mune makama mafi hatsari na hazbullah, kuma muna nan kassammu ne ba zamu bar kasarmu gay an mamaya ba.

Wasu sun bayyana cewa a shirye suke su yi shahada a kan kasarsu da akamamaye, kamar yadda wasu suka yi amma ba zasu taba ja da baya a kan matsayinsu ba.

A cikin wannan halin ne shugaban kasar faransa Emanuel Macron, wanda kumakasarsa na daga cikin kwamitin da aka kafa don kula da aiwatar da yarjeniyar ta tsagaita budewa juna wuta tsakanin kungiyar Hizbullah da kuma HKI na kwanaki 60.

Daga karshe dai HKI da kuma Amurka sun rasa na yi sai suka fara janyewa daga yankun kasar Lebanin da suke mamaye da su, suna ficewa mutane suna komawa cikin gidajensu a yau Litinin.

Manufar HKI na fara yaki da kungiyar Hizbullah da farko shi ne hanata tallafawa ko shi yakin da ake fafatawa da kungiyoyin masu gwagwarmaya da ita a gaza, ba tare da ta shiga cikekken yaki da kungiyar ba, amma ganin yadda dubabban daruruwan yahudawa a arewacin kasar Falasdinu da aka mamaye sun kasa komawa gidajensu a yankin, kuma sun zama matsala ga gwamnatin HKI, wannan yasa ta shiga yankin. Gadangan da kungiyar Hizbullah musamman bayan sun sami nasarar kashe shugaban kungiyar Sayyed Hassan Nasarallh.

Amma karfin sojoji da makaman da Hizbullah ta nuna ya kara dulmuya HKI a cikin karin musiba, don hizbullah sun yi amfani da makamai masu linzami wadanda suke kaiwa har gaba da birnin Tel’aviv, ko yafa. A nan ne HKI taga cewa ba zata iya tahammulin musibun ba, don haka sai Amurka ta aika jakadan zuwa kasar Lebanon wacce ta sami nasaran gamsar da kungiyar

Don haka tsagaita budewa juna wuta a Lebanon bukatar HKI ce, kuma saboda gazwarsu shiga kasar Lebanon da kuma isar makaman Hizbullah zuwa cikin tsakiya da ma kudancin kasar Lebanon, har a wasu lokacinda HKI ta rasa sojoji masu yawa a wasu hare-haren Hizbullah.

Amma bayan an tsagauita wuta ne, sai wasu sojojin HKI suka shiga wasu kauyuwa a kasar ta Lebanon suna nemna makaman kungiyar da kuma irin ramukan da suka gina a karakashin kasa don adana makamansu.

Sannan yanzun kuma an tilasta masi ficewa daga kudancin kasar ta Lebanon, idan suna sun wannan tsgaita wuta ta dore, idan kuma sun yi taurine kai ta kuwa za’a koma gidan jiya.

Masu sauraro karshen sharhin bayan labaran Kenan.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a kudancin kasar Lebanon wadannan yankuna da kungiyar

এছাড়াও পড়ুন:

Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya reshen Jihar Benuwe, a ranar Alhamis, ta bayyana cewa aƙalla shanu 340 na mambobinta ne aka sace a cikin watan Yuli na 2025.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da sakataren ƙungiyar na jiha, Ibrahim Galma ya fitar kuma aka rabawa manema labarai a Makurdi.

Tinubu ya tsawaita wa’adin aikin shugaban hukumar Kwastam Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa

A cewar sanarwar, lamarin ya faru ne a garin Agatu da wasu sassan Ƙaramar hukumar Guma da ke Jihar Benuwe.

Galma ya kuma yi zargin cewa, ɓarayin shanu da ke afkawa jama’a a Ƙaramar hukumar Agatu sun faɗaɗa hare-harensu zuwa sassan Jihar Kogi.

“A ranar 19 ga Yuli, 2025 wasu da ake zargin ’yan ƙabilar unguwar Eguma ne a ƙaramar hukumar Agatu sun sace shanu 73 na wani Sale Abubakar (makiyayi Fulani), kuma har ya zuwa yanzu ba a ƙwato shanun ba.

“A ranar 21/7/2025 wani gungun masu aikata laifuka daga unguwar Agatu sun yi awon gaba da shanu 80 na Ardo Sarkin Fulanin Bagana, an yi awon gaba da shanun ne a Jihar Kogi, kusa da kan iyaka da ƙaramar hukumar Agatu ta Jihar Benuwe.

Ɓarayin sun kwashe shanun zuwa ƙauyukan Agatu. Daga baya kuma, an ƙwato shanu 30 daga cikin 80 a Agatu, inda ba a iya gano 50 ba.

“A ranar 24 ga Yuli, 2025 wasu miyagu matasa ‘yan garin Agatu sun yi awon gaba da wasu shanu 213 na Garah Mobaba, hakan kuma ya faru ne a kan iyaka tsakanin Jihar Kogi da Ƙaramar hukumar Agatu ta Jihar Benuwe, haka kuma lamarin na faruwa a wasu sassan Ƙaramar hukumar Guma ta Jihar Benuwe, inda aka samu rahotannin sace-sacen shanu da kuma kashe-kashen makiyaya.”

Shanun mallakin Sale Abubakar (makiyayin Fulani), kuma har ya zuwa yanzu, ba a ƙwato shanun da aka sace ba.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Haaretz: Sojojin Isra’ila 7 ne suka kashe kansu a watan Yuli
  • Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing
  • Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah
  •  Shugaban Kasar Lebanon Aun Ya Ce Mun Aike Wa  Amurka Sakwanni Akan Dakatar Da Hare-haren HKI
  •  Sojojin Sahayoniya Suna Ci Gaba Da Kisan Kiyashi A Gaza
  • Dalilan Da Suka Sa Canada Ta Goyi Bayan Kafa Kasar Falasɗinu
  • Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine
  • Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku  
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa