Sharhin Bayan Labarai: Jajircewar Mutanen Kasar Lebanon A Gaban Sojojin Mamaya A Kudancin Kasar
Published: 27th, January 2025 GMT
Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka, Sharhin bayan labarammu zai yi magana a kan “jajircewar mutanen kudancin kasar Lebanon fuskantar sojojin HKI’ yan mamaya’ wanda ni tahir amin.
///…A Jiya lahadi be wa’adin ficewar HKI daga yankuna da garuruwan da suka mammaye a kudancin kasar Lebanon, amma karfe 4 da safe yana cika mutanen wadannan yankuna suka kwarara zuwa gidajensi, amma ko da suka isa sai suka ga cewa sojojin kasar Lebanon sun sha shinge don hana mutane wucewa zuwa wadannan wurare, don har yanzun akwai sojojin HKI a yankin suna iya kashe su.
Banda haka sojojin HKI sun kara wayoyin wasu daga cikin mutanen wadannan yankuna, suna fada masu cewa kada su kuskura su shiga wadannan yankuna.
Amma sai jerin gwanon mutoci da barbura da mutane masu takawa da kafa kake gani suna kwarara zuwa gidajensu. Gwamnatin kasar Amurka ta bukaci gwamnatin Lebanon su amince a kara lokacin janyewar sojojin HKI daga wadannan yankuna na kudancin kasar Lebanon, har zuwa 18 ga watan Fabrayru mai zuwa, amma gwamnatin ta ki amincea da hakan.
A jiya Lahadi sojojin HKI sun bude wuta kan wasu mutanen kudancin kasar Lebanon wadanda suke son komawa gidajensu, inda suka kashe mutane 18 suka kuma raunata wasu kimani 100 a yankunan daban daban da suke mamaye da su a kasar ta Lebanon.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ya nakalto yadda al-amura suka tafiya a kudancin kasar Lebanon a safiyar ranar litinin, inda wasu suke cewa, ai mune makama mafi hatsari na hazbullah, kuma muna nan kassammu ne ba zamu bar kasarmu gay an mamaya ba.
Wasu sun bayyana cewa a shirye suke su yi shahada a kan kasarsu da akamamaye, kamar yadda wasu suka yi amma ba zasu taba ja da baya a kan matsayinsu ba.
A cikin wannan halin ne shugaban kasar faransa Emanuel Macron, wanda kumakasarsa na daga cikin kwamitin da aka kafa don kula da aiwatar da yarjeniyar ta tsagaita budewa juna wuta tsakanin kungiyar Hizbullah da kuma HKI na kwanaki 60.
Daga karshe dai HKI da kuma Amurka sun rasa na yi sai suka fara janyewa daga yankun kasar Lebanin da suke mamaye da su, suna ficewa mutane suna komawa cikin gidajensu a yau Litinin.
Manufar HKI na fara yaki da kungiyar Hizbullah da farko shi ne hanata tallafawa ko shi yakin da ake fafatawa da kungiyoyin masu gwagwarmaya da ita a gaza, ba tare da ta shiga cikekken yaki da kungiyar ba, amma ganin yadda dubabban daruruwan yahudawa a arewacin kasar Falasdinu da aka mamaye sun kasa komawa gidajensu a yankin, kuma sun zama matsala ga gwamnatin HKI, wannan yasa ta shiga yankin. Gadangan da kungiyar Hizbullah musamman bayan sun sami nasarar kashe shugaban kungiyar Sayyed Hassan Nasarallh.
Amma karfin sojoji da makaman da Hizbullah ta nuna ya kara dulmuya HKI a cikin karin musiba, don hizbullah sun yi amfani da makamai masu linzami wadanda suke kaiwa har gaba da birnin Tel’aviv, ko yafa. A nan ne HKI taga cewa ba zata iya tahammulin musibun ba, don haka sai Amurka ta aika jakadan zuwa kasar Lebanon wacce ta sami nasaran gamsar da kungiyar
Don haka tsagaita budewa juna wuta a Lebanon bukatar HKI ce, kuma saboda gazwarsu shiga kasar Lebanon da kuma isar makaman Hizbullah zuwa cikin tsakiya da ma kudancin kasar Lebanon, har a wasu lokacinda HKI ta rasa sojoji masu yawa a wasu hare-haren Hizbullah.
Amma bayan an tsagauita wuta ne, sai wasu sojojin HKI suka shiga wasu kauyuwa a kasar ta Lebanon suna nemna makaman kungiyar da kuma irin ramukan da suka gina a karakashin kasa don adana makamansu.
Sannan yanzun kuma an tilasta masi ficewa daga kudancin kasar ta Lebanon, idan suna sun wannan tsgaita wuta ta dore, idan kuma sun yi taurine kai ta kuwa za’a koma gidan jiya.
Masu sauraro karshen sharhin bayan labaran Kenan.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a kudancin kasar Lebanon wadannan yankuna da kungiyar
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha
Gwamnatin kasar Iran ta bayyana wasu abubuwan da bata amince da su ba, a jawabin bayan taro na musamman na kungiyar kasashen musulmi ta (OIC) wanda aka gudanar a birnin Doha na kasar Qatar a ranar litinin 15 gawatan Satumba da mukeciki. Sannan ta kara tabbatar da goyon bayanta ga gwagwarmayan da Falasdinawa suke yi da HKI don kwatar kasarsu da ta mamaye.
A cikin wani bayanin da ma’aikatar harokokin wajen kasar Iran ta fitar a yau Laraba, Jumhuriyar Musulunci ta Iran, tana kara jaddada goyon bayanta ga al-ummar Falasdina, kuma tana kara jaddada tir da allawai da kissan kiyashin da HKI take yi a Gaza da kuma sauran yankunan falasdinawa da ta mamaye. Kuma tana godewa mutanen kasar Iran dangane da goyon bayan da suke bawa Falasdinawa a gwagwarmayansu da HKI.
Dangane da shawarorin da aka gabatar a taron OIC, Iran tana godiya kasashen musulmi da wadanda ba musulmi kan shawarorin da suka gabatar, don warware rikicin Falasdinawa, daga ciki har da “New York Declaration” ta samar da kasashe 2. Da wasu da dama. Amma JMI tana ganin kafa kasashe biyu bazai warware rikicin ba. Tana ganin gudanar da zaben raba gardama, a kasar wanda zai hada da dukkan falasnawa a ko ina suke a ciki da wajen kasar, don zabawa kansu tsari dairin gwamnati da suke su ta demucradiyya. Irab tana ganin samar da kasar Falasdinu a dukkan fadinkasar wacce take da dukkan birnin Qudus a matsayin babban birnin kasar ita ce mafita. Yahudawan da suke son zama su zauna wadanda suke son tafiya su koma kasarsu ta asalali.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Chadi: Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa September 17, 2025 Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila September 17, 2025 Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza September 17, 2025 Iran da Saudiyya sun bukaci hadin kan Musulmi game da halin da ake a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci