Karya ta kai kwikwiyonta mara lafiya asibiti
Published: 26th, January 2025 GMT
A kwanakin nan ne wani asibitin kula da dabbobi a kasar Turkiyya ya wallafa wani labari mai ratsa jiki na wata karya da ba ta da masauki ta ɗauki ɗanta da ya suma a bakinta ta ajiye shi a kofar asibitin kamar mai neman taimako.
Idan ba don gajeran bidiyon da kyamarorin na’urar CCTV suka ɗauka ba, da alama yawancin mutane za su yi tunanin wannan labarin ba zai iya zama gaskiya ba.
Wani asibitin dabbobi a Unguwar Adnan Kahveci da ke Beylikduzu, a lardin Istanbul na ƙasar Turkiyya, kwanan ya fitar da rahoton ɗaya daga cikin muhimman harkokin asibitin.
A ranar 13 ga watan Janairu, wani masoyin dabbobi ya kawo wani matashin kwikwiyo da suka same shi a kan titi, yana mai cewa shi kaɗai ne ya tsira daga cikin sauran ’yan uwansa.
Jami’an asibitin sun ruga don yi wa ɗan kwikwiyon magani sai ga wata karya ta fito daga bakin ƙofa da wani kwikwiyo a sume a bakinta.
Wani masani ne ya lura da wannan dabbar da ta ƙaurace masa, sai ya garzaya domin ya kula da ’ya’yanta, waɗanda ke fama da rashin lafiya kuma jikinta ya yi rauni sosai.
Kyamarorin sa-ido daga cikin asibitin sun nuna mahaifiyar kwikwiyon da ke cikin damuwa tana bin likitocin dabbobi zuwa asibitin kuma ta zuba musu ido, yayin da suke kula da jaririnta da ya suna.
An yi sa’a, Dakta Baturalp Oghan da tawagarsa sun sami damar ceton ɗan kwikwiyon kuma yanzu dukan karnukan suna murmurewa a asibitin.
“Komai na tafiya yadda ya kamata. Maganin da ake yi wa kwikwiyon da dan’uwansa zai ci gaba na ɗan lokaci kaɗan.
“A wannan lokacin, ba ma karɓar bakin marasa lafiya saboda kula da lafiyarsu,” in ji Dokta Oghan.
“Mahaifiyar karyar tana samun sauƙi sosai. Labarinta ya birge mutane da yawa, karyar tana da basira da kulawa.
“Tana nuna irin soyayyar da uwa karya take yi wa ’ya’yanta.”
A bayyane yake, nonon mahaifiyar ba ya isa ta ci gaba da shayar da sauran ’ya’yanta gaba ɗaya, wanda shi ne dalilin da ya sa wasu ’yan kwikwiyon suka mutu cikin rashin shayarwar, don haka asibitin yana kara kula da ’yan kwikwiyon da suka tsira da ransu da taimakon ciyar da su.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
Daga Usman Muhammad Zaria
Majalisar Zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da bayar da rancen kudi ga hukumar gidaje ta jihar domin gina gidaje 52 a Dutse.
A cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ya fitar, ya bayyana cewa gidajen za su kunshi masu dakuna uku da kuma dakuna biyu kowanne.
Ya ce aikin zai kasance a gaban tsohuwar unguwar majalisar dokoki, kusa da hanyar wucewa ta Jami’ar Tarayya da je Dutse, a matsayin wani shiri na asusun gina gidaje karkashin ma’aikatar gidaje, ci gaban birane da tsare-tsaren yankuna, ta hannun hukumar gidaje ta jihar.
Alhaji Sagir ya bayyana cewa, wannan mataki na nuna kudirin gwamnati wajen magance matsalar gidaje a babban birnin jihar, kara habaka ci gaban birane, tare da samar da ayyukan yi ga matasan jihar.
Ya ce an tsara wannan asusu ne domin tabbatar da dorewa, ta yadda za a ci gaba da zuba jari a ayyukan samar da gidaje masu araha a fadin jihar.
Haka kuma ya kara da cewa, gwamnatin jihar tana da kudirin ci gaba da inganta rayuwar al’ummarta, ta hanyar ayyuka masu amfani da jama’a, da ke inganta walwala, karfafa tattalin arziki, da tallafa wa matasa.
Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, majalisar ta amince da bayar da kwangilar gyara da inganta gidan baki guda biyu (Malam Adamu Chiroma House da kuma Senator Francis Ella House) da ke cikin G9 Quarters a Dutse, da kudin sama da naira miliyan 219.7.
Ya ce aikin zai haɗa da cikakken gyara da inganta gine-ginen, gyaran hanyoyin ruwa da kuma girka tankokin ruwa ga kowanne daga cikin gidajen biyu.
Ya ce hakan na da nufin tabbatar da wadataccen ruwan sha mai dorewa a wuraren.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya kara da cewa, amincewar da aka yi da wannan kwangila na nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen kula da dukiyar jama’a da kuma tabbatar da cewa gine-ginen gwamnati suna cikin yanayi mai kyau da nagarta.