Aminiya:
2025-06-27@14:01:29 GMT

Karya ta kai kwikwiyonta mara lafiya asibiti

Published: 26th, January 2025 GMT

A kwanakin nan ne wani asibitin kula da dabbobi a kasar Turkiyya ya wallafa wani labari mai ratsa jiki na wata karya da ba ta da masauki ta ɗauki ɗanta da ya suma a bakinta ta ajiye shi a kofar asibitin kamar mai neman taimako.

Idan ba don gajeran bidiyon da kyamarorin na’urar CCTV suka ɗauka ba, da alama yawancin mutane za su yi tunanin wannan labarin ba zai iya zama gaskiya ba.

’Yan bindiga sun sace mutum 22 a ƙauyukan Kaduna Shin wannan ce kaka mafi muni ga Man-United a Gasar Firimiya?

Wani asibitin dabbobi a Unguwar Adnan Kahveci da ke Beylikduzu, a lardin Istanbul na ƙasar Turkiyya, kwanan ya fitar da rahoton ɗaya daga cikin muhimman harkokin asibitin.

A ranar 13 ga watan Janairu, wani masoyin dabbobi ya kawo wani matashin kwikwiyo da suka same shi a kan titi, yana mai cewa shi kaɗai ne ya tsira daga cikin sauran ’yan uwansa.

Jami’an asibitin sun ruga don yi wa ɗan kwikwiyon magani sai ga wata karya ta fito daga bakin ƙofa da wani kwikwiyo a sume a bakinta.

Wani masani ne ya lura da wannan dabbar da ta ƙaurace masa, sai ya garzaya domin ya kula da ’ya’yanta, waɗanda ke fama da rashin lafiya kuma jikinta ya yi rauni sosai.

Kyamarorin sa-ido daga cikin asibitin sun nuna mahaifiyar kwikwiyon da ke cikin damuwa tana bin likitocin dabbobi zuwa asibitin kuma ta zuba musu ido, yayin da suke kula da jaririnta da ya suna.

An yi sa’a, Dakta Baturalp Oghan da tawagarsa sun sami damar ceton ɗan kwikwiyon kuma yanzu dukan karnukan suna murmurewa a asibitin.

“Komai na tafiya yadda ya kamata. Maganin da ake yi wa kwikwiyon da dan’uwansa zai ci gaba na ɗan lokaci kaɗan.

“A wannan lokacin, ba ma karɓar bakin marasa lafiya saboda kula da lafiyarsu,” in ji Dokta Oghan.

“Mahaifiyar karyar tana samun sauƙi sosai. Labarinta ya birge mutane da yawa, karyar tana da basira da kulawa.

“Tana nuna irin soyayyar da uwa karya take yi wa ’ya’yanta.”

A bayyane yake, nonon mahaifiyar ba ya isa ta ci gaba da shayar da sauran ’ya’yanta gaba ɗaya, wanda shi ne dalilin da ya sa wasu ’yan kwikwiyon suka mutu cikin rashin shayarwar, don haka asibitin yana kara kula da ’yan kwikwiyon da suka tsira da ransu da taimakon ciyar da su.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Da yake gabatar da kudirin, dan majalisar, Abdullahi ya nuna matukar damuwarsa kan kisan da aka yi wa matafiyan a ranar Juma’a, a lokacin da suka bata kan hanyarsu a yayin da suke tafiya don halartar wani daurin aure a karamar hukumar Mangu.

 

Ya ce, wadanda aka kashen, ba su dauke da wani makami, kawai suna kan hanyarsu ne ta zuwa daurin aure, wasu da ba a san ko su wanene ba suka kai musu hari tare da kashe su, lamarin da ya jefa ‘yan uwan matafiyan cikin jimami.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ribas: Duk wani rikici tsakanina da Fubara ya ƙare – Wike
  • NDLEA ta kafa cibiyar kula da masu shaye-shaye a Yobe 
  • Sanatan Neja Ta Arewa Ya Yi Allah Wadai Da Kashe Sojoji A Mariga
  • Yadda na kuɓuta daga harin Filato — Wani mutum
  • ’Yan bindiga sun kashe ɗan sanda, sun jikkata wasu 3 a Zariya
  • Bello Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a Zamfara
  • Bejjo Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a Zamfara
  • Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato
  • Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027
  • Harin asibiti ya kashe mutum 40 a Sudan — WHO