Amurka ta hau kujerar-na-ƙi kan buƙatar MDD ta tsagaita wuta a Gaza
Published: 19th, September 2025 GMT
Ƙasar Amurka ta hau kujerar-na-ƙi kan wani ƙudurin Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ke neman a dakatar da yaki a Gaza nan take kuma ba tare da sharaɗi ba.
Daftarin kudurin na majalisar ya kuma buƙaci Isra’ila ta cire duk wani takunkumi kan kai agaji ga yankin na Falasɗinawa.
Wani ya sace munduwar Fir’auna a gidan tarihin Masar Kasar Albania ta nada mutum-mutumi a matsayin ministaKudurin, wanda ƙasashe 10 da aka zaɓa daga cikin mambobi 15 na majalisar suka tsara, ya kuma buƙaci a saki dukkan fursunonin aka yi garkuwa da su daga hannun Hamas da sauran kungiyoyi ba tare da sharadi ba, cikin mutunci da girmamawa.
Kudurin dai ya samu goyon bayan ƙasashe 14, sai dai Amurka ta yi amfani da karfin tuwo wajen kin amincewa da shi.
Wannan shi ne karo na shida da Amurka ke hawa kujerar-na-ki kan batun yaki tsakanin Isra’ila da Hamas tun kusan shekaru biyu da suka gabata.
Jakadiyar Denmark a Majalisar Dinkin Duniya, Christina Markus Lassen, kafin ta kada kuri’arta, ta ce, “An tabbatar da yunwa a Gaza, ba hasashe ba ne, ba jita-jita ba, an tabbatar da ita.”
Ta ƙara da cewa: “Isra’ila ta faɗaɗa hare-haren soji a birnin Gaza, lamarin da ke ƙara jefa fararen hula cikin wahala. Wannan mummunan yanayi da gazawar jin kai ne ya tilasta mu daukar mataki a yau.”
Wani rahoto daga hukumar da ke sa ido kan yunwa a duniya ya tabbatar da cewa birnin Gaza da kewaye na fama da yunwa, kuma akwai yiwuwar ta yadu.
Amurka na da al’adar kare Isra’ila a Majalisar Dinkin Duniya. Sai dai a makon da ya gabata, a wani mataki da ba kasafai ake gani ba, ta goyi bayan wata sanarwa daga majalisar da ke sukar hare-haren da aka kai Qatar, duk da cewa ba a ambaci Isra’ila a cikin rubutun ba.
Wannan mataki ya nuna goyon bayan Shugaban Amurka Donald Trump ga umarnin da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya bayar.
Sai dai hawa kujerar-na-kin da Amurka ta yi a ranar Alhamis ya sake tabbatar da cewa Washington na ci gaba da ba Isra’ila kariya ta diflomasiyya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Isra ila Majalisar Dinkin Duniya tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
A yayin da ake ci gaba da cece-kuce kan kalaman Shugaban Amurka Donald Trump da ke zargin gwamnatin Nijeriya da watsi da batun kisan Kiristoci a ƙasar, Ma’aikatar Yaƙin Amurka ta bayyana cewa ta fara shirin kai farmaki a Nijeriya.
Sakataren Ma’aikatar, Pete Hegseth, ne ya tabbatar da hakan cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Asabar, yana mai cewa ma’aikatarsa “na shirye-shiryen ɗaukar mataki” bayan umarnin da Trump ya bayar.
Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya“Muna shirye-shirye don ɗaukar mataki a Nijeriya. Idan gwamnatin Nijeriya ba ta kare Kiristoci ba, za mu kai hari, mu kawar da ‘yan ta’addan Musulmai da ke aikata wannan ta’asar,” in ji Hegseth.
Trump dai ya yi wannan barazanar ne a cikin wani saƙo da ya wallafa a Truth Social, inda ya ce Amurka za ta dakatar da duk tallafin da take bai wa Nijeriya, kuma tana iya “shiga ƙasar da ƙarfin soji domin share ‘yan ta’addan da ke kashe Kiristoci.”
“Idan gwamnatin Nijeriya ta ci gaba da bari ana kashe Kiristoci, Amurka za ta dakatar da duk wata tallafi, kuma mai yiwuwa ta shiga wannan ƙasar, ta cike da ƙarfin gwiwa domin kawar da ’yan ta’addan Musulmai masu zafin kishin addini,” in ji Trump.
Ya kuma gargaɗi gwamnatin Nijeriya da ta gaggauta ɗaukar mataki, yana cewa idan Amurka ta kai farmaki “za ta yi shi cikin sauri, da tsananin ƙarfi, da gamsuwa.”
Lamarin na zuwa ne kwana guda bayan Trump ya mayar da Nijeriya cikin jerin ƙasashen da za a sanyawa ido, yana zargin cewa “ana yi wa Kiristoci kisan gilla” a hannun ƙungiyoyin Musulmi masu tsattsauran ra’ayi.
Sai dai a martanin da ya mayar, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ce Nijeriya tana nan daram a matsayin ƙasa mai dimokuraɗiyya wadda kundin tsarin mulkinta ke tabbatar da ‘yancin yin addini da haƙuri tsakanin mabambantan addinai.
“Tun daga shekarar 2023, gwamnatinmu tana gudanar da tattaunawa sosai da shugabannin addinai na Kiristanci da Musulunci, tare da ci gaba da magance matsalolin tsaro da ke shafar ‘yan ƙasa daga addinai da yankuna daban-daban,” in ji Tinubu.
A cewar mai ba wa Tinubun shawara na musamman kan yaɗa manufofi, Daniel Bwala, za a yi ganawa tsakanin Shugaba Tinubu da Shugaba Trump “a cikin kwanaki kaɗan masu zuwa” domin tattaunawa da warware wannan saɓanin fahimta.