Aminiya:
2025-09-19@07:21:39 GMT

Amurka ta hau kujerar-na-ƙi kan buƙatar MDD ta tsagaita wuta a Gaza

Published: 19th, September 2025 GMT

Ƙasar Amurka ta hau kujerar-na-ƙi kan wani ƙudurin Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da ke neman a dakatar da yaki a Gaza nan take kuma ba tare da sharaɗi ba.

Daftarin kudurin na majalisar ya kuma buƙaci Isra’ila ta cire duk wani takunkumi kan kai agaji ga yankin na Falasɗinawa.

Wani ya sace munduwar Fir’auna a gidan tarihin Masar Kasar Albania ta nada mutum-mutumi a matsayin minista

Kudurin, wanda ƙasashe 10 da aka zaɓa daga cikin mambobi 15 na majalisar suka tsara, ya kuma buƙaci a saki dukkan fursunonin aka yi garkuwa da su daga hannun Hamas da sauran kungiyoyi ba tare da sharadi ba, cikin mutunci da girmamawa.

Kudurin dai ya samu goyon bayan ƙasashe 14, sai dai Amurka ta yi amfani da karfin tuwo wajen kin amincewa da shi.

Wannan shi ne karo na shida da Amurka ke hawa kujerar-na-ki kan batun yaki tsakanin Isra’ila da Hamas tun kusan shekaru biyu da suka gabata.

Jakadiyar Denmark a Majalisar Dinkin Duniya, Christina Markus Lassen, kafin ta kada kuri’arta, ta ce, “An tabbatar da yunwa a Gaza, ba hasashe ba ne, ba jita-jita ba, an tabbatar da ita.”

Ta ƙara da cewa: “Isra’ila ta faɗaɗa hare-haren soji a birnin Gaza, lamarin da ke ƙara jefa fararen hula cikin wahala. Wannan mummunan yanayi da gazawar jin kai ne ya tilasta mu daukar mataki a yau.”

Wani rahoto daga hukumar da ke sa ido kan yunwa a duniya ya tabbatar da cewa birnin Gaza da kewaye na fama da yunwa, kuma akwai yiwuwar ta yadu.

Amurka na da al’adar kare Isra’ila a Majalisar Dinkin Duniya. Sai dai a makon da ya gabata, a wani mataki da ba kasafai ake gani ba, ta goyi bayan wata sanarwa daga majalisar da ke sukar hare-haren da aka kai Qatar, duk da cewa ba a ambaci Isra’ila a cikin rubutun ba.

Wannan mataki ya nuna goyon bayan Shugaban Amurka Donald Trump ga umarnin da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya bayar.

Sai dai hawa kujerar-na-kin da Amurka ta yi a ranar Alhamis ya sake tabbatar da cewa Washington na ci gaba da ba Isra’ila kariya ta diflomasiyya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Isra ila Majalisar Dinkin Duniya tabbatar da

এছাড়াও পড়ুন:

Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono

Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Ondo ta tabbatar da kama wata mata mai suna Iluyemi Bosede bisa zargin kashe yayarta, Tewogboye Omowumi, a Akure, babban birnin jihar.

A cewar sanarwar da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, Olayinka Ayanlade, ya fitar a ranar Talata, ya ce lamarin ya faru ne a ranar shida ga Satumba, 2025, bayan wata sa’insa da ta kaure tsakanin matar da marigayiyar kan Naira 800.

Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya

Jami’in ya bayyana cewa Bosede ta ture ’yar uwarta har ta faɗi ƙasa, lamarin da ya haifar da mutuwarta.

Ya ce, “Binciken farko ya nuna cewa Iluyemi Bosede ta je wurin yayar tata, Tewogboye Omowumi mai shekaru 35, domin karbar bashinta na N800 na kudin tumatir da barkono. Sai dai tankiyar da ta fara a matsayin ƙaramin sabani ta rikide zuwa tashin hankali, inda ake zargin Bosede ta riƙe kayan marigayiyar har ta faɗi ƙasa.”

“Abin takaici, duk da an garzaya da marigayiyar asibiti don samun kulawar gaggawa, likitoci sun tabbatar da mutuwarta tun kafin a fara ba ta taimako. Wannan lamari ya nuna yadda ƙaramin sabani zai iya rikidewa zuwa mummunar husuma idan ba a magance shi cikin lumana ba.”

Bayan faruwar lamarin, rundunar ta ce ta kama wadda ake zargi kuma tana tsare da ita a halin yanzu, yayin da bincike ke ci gaba.

Rundunar ta kuma tabbatar da cewa za a gurfanar da wadda ake zargin a gaban kotu bayan kammala bincike, domin ta girbi abin da ta shuka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Yi Amfani Da Kujeran Veto Don Hana Zaman Lafiya A Gaza
  • ’Yan sanda sun kama mutum 9 kan yin garkuwa da kansu
  • Isra’ila na ci gaba da ragargaza Birnin Gaza ta sama da ƙasa
  • Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Gumi
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
  • Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote