Aminiya:
2025-11-03@16:05:37 GMT

Gwamnatin Kano za ta sake yi wa zawarawa da ’yan mata auren gata

Published: 2nd, September 2025 GMT

Gwamnatin Kano ta sanar da cewa tana shirye-shiryen gudanar da auren zawarawa da ’yan mata, wanda ya zarce na baya da ta yi.

Babban Kwamanda Hisbah na Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ne bayyana hakan a yayin ziyarar gaisuwa da ya kai wa Fadar Sarkin Rano a ranar Litinin.

Zabarmawa Sun Bayyana Dalilin Bai wa Gwamnan Kebbi Sarautar Garkuwa Cibiyar Ayyukan Daular Usmaniyya za ta karrama Sarkin Zazzau

Sheikh Daurawa ya ce a wannan karon angwaye da amaren za su mori gwaggwaban tanadi na musamman daga Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf.

Ana iya tuna cewa, a watan Oktoban 2023 ne Gwamnatin Kano ta ɗaura auren mata 1,800 da angwayensu 1,800 wanda ta ɗauki watanni tana shiryawa.

Tun bayan hawansa mulki ne, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanar da cewa zai yi wa matan da ba su da galihu auren gata, ta hanyar samar musu da dukkan kayayyakin da mace ke bukata a gidan aure da kuma yi musu walicci.

A wancan lokacin, ɗaura aurarrakin ne a wasu masallatan Juma’a a dukkan ƙananan hukumomi 44 da ke faɗin jihar.

A babban Masallacin Juma’a na gidan Sarkin Kano kawai an daura auren kusan mutum 300 wanda shi ne Gwamna Abba Kabir Yusuf da Shugaban Hisbah Sheikh Daurawa, wanda shi ne jagoran hidimar suka halarta.

Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ne ya yi walicin angwaye yayin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya zama waliyyin amare a kan sadaki Naira 50,000 ga kowace amarya.

Gwamnan Jigawa Umar Namadi na daga cikin waɗanda suka harlaci daurin auren.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: auren zawarawa Jihar Kano Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa

এছাড়াও পড়ুন:

Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 

 

Kwankwaso, wanda shi ne dan takarar shugaban kasa na NNPP a zaben 2023, ya fitar da wata sanarwa mai karfi yana gargadin cewa kalaman Trump na iya kara ruruta wutar rikicin addini da kuma kara ta’azzara rashin tsaro a kasar.

 

A shafinsa na X, tsohon gwamnan ya yi Allah-wadai da matakin Trump na ayyana Nijeriya a matsayin “kasar da ke da matukar damuwa,” wanda kuma ya yi zargin ikirarin “kisan kare dangi ga Kiristoci.”

 

Kwankwaso, ya yi kira ga Amurka da ta taimaka wa Nijeriya da tallafin fasaha da leƙen asiri maimakon barazana, sannan ya shawarci Gwamnatin Tarayya da ta zurfafa hulɗar diflomasiyya ta hanyar naɗa wakilai na musamman domin tattaunawa.

 

“Ga ‘yan uwana ‘yan ƙasa, wannan muhimmin lokaci ne da ya kamata mu jaddada haɗin kai maimakon rarrabuwar kawuna. Allah ya albarkaci Nijeriya,” in ji Kwankwaso.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi November 3, 2025 Manyan Labarai Kwankwaso Ya Gargaɗi Trump Kan Barazana Ga Nijeriya November 2, 2025 Manyan Labarai Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mayar Da Martani Kan Barazanar Amurka Ga Nijeriya: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yaba Wa Kwankwaso 
  • Uwargidan Gwamnan  Zamfara Ta Yaba Wa  Karamar Hukumar Gusau Bisa Shirin Tallafawa Jama’a
  • Hamas Ta yi Watsi Da Zargin Da Amurka Tayi Mata Kan Batun Motocin Agaji A Gaza
  • Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan: Mayakan RSF Sun Kashe Mata 300 Da Yi Wa 25 Fyade A El Fasher
  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai