Aminiya:
2025-09-17@21:51:41 GMT

Zabarmawa Sun Bayyana Dalilin Bai wa Gwamnan Kebbi Sarautar Garkuwa

Published: 2nd, September 2025 GMT

Kungiyar Zabarmawa ta Najeriya ta karrama Gwamnan Jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris, da sarautar Garkuwan Zabarmawa, saboda gudummawar da ya bayar wajen ci gaban al’umma da tallafa wa ƙungiya.

Da yake bayyana dalilin bai wa gwamnan sarautar a madadin shugaban ƙungiyar na ƙasa, Sarkin Zabarmawa, Alhaji Bello Zabarmawa, ya ce: “An ba da wannan sarauta ne domin nuna gamsuwa da irin ci gaban da Gwamna Idris ya kawo wa talakawa.

Cibiyar Ayyukan Daular Usmaniyya za ta karrama Sarkin Zazzau Gwamnatin Tarayya ta ɓullo da sabon manhajin karatun firamare da sakandire

“Mun tuntubi mutane da yawa kafin a zaɓe shi, kuma kowa ya tabbatar cewa shi ya cancanta.”

A nasa jawabin, Sarkin Zabarmawa na Jihar Kebbi, wanda kuma shi ne tsohon shugaban majalisar dokokin jihar, Abdulmuminu Kamba, ya yaba da irin goyon bayan da gwamnan ke bai wa ƙungiyar da kuma al’ummar jihar.

Shi ma Gwamna Idris, bayan godewa ƙungiyar, ya bayyana cewa wannan karramawar za ta ƙara masa kwarin gwiwa.

“Na yi alƙawari gwamnatina ta talakawa ce. Zan ci gaba da yin iya ƙoƙarina wajen tallafa wa mutanen Jihar Kebbi da kuma kare martabar wannan sarauta da aka damƙa min,” in ji shi.

Kabilar Zabarmawa, wadda aka fi sani da Zabarmawa ko Zabaruma, na daga cikin manyan ƙabilu a Najeriya da Jamhuriyar Nijar, inda suka shahara wajen kasuwanci da jajircewa a fannin neman arziki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Garkuwan Zabarmawa Jihar Kebbi Zabarmawa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

Ya ce ya sayi layin wayar ne daga hannun wani Audu, ɗan kungiyar Vikings wanda ya tsere yanzu.

A wani lamari kuma, ‘yansanda sun kama wasu mutum huɗu da suka shiga gonar wani mutum a Lapai Gwari, inda suka saci kifi da darajar kuɗinsu ta kai Naira 750,000.

Babban wanda ake zargi, Hussaini Garba, ya amsa laifi tare da bayyana Ahmed Yusuf, Ibrahim Musa da Abdulazeez Bawa a matsayin mutanen da suke sayen kifin idan ya sato.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha