Kisan Isuhu Yellow: ’Yan bindiga sun kai harin ɗaukar fansa
Published: 8th, April 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga a ranar Lahadin da ta gabata sun kai harin ɗaukar fansar kashe ƙasurgumin ɗan ta’addan nan, Kachalla Isuhu Yellow da aka fi sani da Ɗan Isuhu.
’Yan ta’addan sun kai harin ne ƙauyen Keta da ke Ƙaramar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara, domin ɗaukar fansar kashe jagoransu da jami’an tsaro suka yi makonni biyu da suka gabata.
Mazauna sun ce maharan sun kashe mutum ɗaya yayin da suka ƙone motoci 11 sannan kuma suka wawushe kayayyaki a kantinan ’yan kasuwa a yayin harin.
Bayanai sun ce ana zargin ’yan ta’addan da suka kai wannan hari mayaƙan Adamu Aliero ne — yayan marigayi Ɗan Isuhu.
Kachalla Yellow wanda ake alaƙantawa da kai munanan hare-hare a Zamfara da kuma babbar hanyar Funtua zuwa Gusau, ya gamu da ƙarshensa ne a yayin wani artabu da wata rundunar haɗin gwiwa ta Asakarawan Zamfara da kuma jami’an ’yan sanda a ƙauyen Keta.
A yayin da wasu rahotanni ke cewa, Ɗan Isuhu ya yi gamo da ƙarshensa ne a hannun wasu ’yan ta’adda masu adawa da shi da ke yi wa Dogo Gide mubaya’a, wasu kuma na cewa dakarun soji ne suka kawar da shi daga doron ƙasa.
Wani mazauni Danjigba — wani yanki da ke makwabtaka da Keta — ya tabbatar da cewa an kashe Isuhu Yellow ne a yayin da yake yunƙurin yi wa jami’an tsaro kwanton ɓauna a hanyarsu ta zuwa ƙauyen Keta domin kai ɗauki.
“Shi da mayaƙansa sun yi ƙoƙarin yi wa jami’an tsaron kwanton ɓauna amma a yayin musayar wuta da su aka kashe shi tare da mayaƙansa da dama.”
Ya ƙara da cewa, ragowar ’yan ta’adda a hanyarsu ta tserewa sun kai wa mazauna Danjigba hari, inda suka kashe mutum takwas ciki har da wani ɗan uwansa da wawushe kuɗi a hannun ’yan kasuwa.
Duk da aukuwar wannan hari, sai dai mazauna suka yi murnar mutuwar Isuhu Yellow, suna masu bayyana shi a matsayin marar imani wanda ya ɗauki alhakin sacewa da zubar da jinin mutane da dama a Tsafe, Gusau, Dan Sadau da kuma Funtua.
Kakakin rundunar ’yan sandan Zamfara, DSP Yazid Abubakar, ya tabbatar da kashe Isuhu Yellow a wani aikin haɗin gwiwa na jami’an tsaro da suka daƙile harin da aka kai ƙauyen Keta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Jihar Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin Sahayoniya Suna Ci Gaba Da Kisan Kiyashi A Gaza
A daidai lokacin da yakin Gaza yake cika kwanaki 664, sojojin HKI suna ci gaba da kisan kiyashi akan Falasdinawan da suke fama da yunwa saboda karancin abinci.
A jiya kadai sojojin mamayar sun yi wa Falasdinawa 80 kisan kiyashi.
Asibitocin yankin Gaza sun sanar da karbar gawawwakin shahidai a jiya da kuma yau Alhamis.
A gefe daya, manzon Amurka Steve Vittkov zai ziyarci HKI a yau Alhamis domin tattauna halin da ake ciki a yankin Gaza.
Wannan ziyarar tashi dai tana zuwa ne a daidai lokacin da majiyoyin ‘yan sahayoniyas suke Magana akan kara daukar matakai masu tsanani akan al’ummar Gaza da yunwa ta jigata su.
A can yankin yammacin Kogin Jordan kuwa wani Bafalasdine ya yi sahahda, yayin da wasu masu yawa su ka jikkata sanadiyyar hare-haren ‘yan share wuri zauna a kusa da garin Ramallah.
Al’ummar Gaza dai suna cikin wahala mai tsanani saboda kisan kiyashin da ‘yan sahhayoniya suke yi musu fiye da shekaru biyu, sannan kuma da jefa su cikin yunwa da su ka yi.
A kowace rana ta Allah, mutanen Gaza suna yin shahada saboda rashin abinci, musamman kananan yara, bayan ga kisan kiyashin da ake yi musu. Mafi karancin Falasdinawa da HKI take kashewa a kowace rana suna a tsakanin 80 zuwa 100.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kassim: Duk Wanda Yake Neman Hizbullah Ta Ajiye Makamanta Yana Yi Wa Isra’ila Aiki July 31, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata July 31, 2025 Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila July 31, 2025 Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba July 31, 2025 Sojan Amurka Ya Bada Ruwayar Yadda Sojojin Sahayoniyya Suka Kashe Wani Yaro Balasdine July 31, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku July 31, 2025 Qolibaf: Barin HKI Ta Yi Abinda Taga Dama Ne Yana Karfafa Mata Giwa July 30, 2025 Yunwa Ta Kashe Karin Falasdinawa 7 A Gaza July 30, 2025 Malta Zata Amince da Samuwar Falasdinu a Cikin Watan Satumba Mai Zuwa July 30, 2025 Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah July 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci