HausaTv:
2025-07-06@20:55:04 GMT

Madagascar ta kawo karshen cutar shan inna a tsibirin

Published: 22nd, May 2025 GMT

Hukumar lafiya ta duniya ta sanar da cewa an kawo karshen cutar shan inna, mai nakasa yara a Madagascar.

Tun daga shekara ta 2020, tsibirin ke fuskantar karuwar nau’in cutar shan inna na 1, da har yanzu ke yaduwa.

Wakiliyar UNICEF a Madagascar, Christine Jaulmes, ta yi farin ciki da matakin.

UNICEF ta ce manyan matakan gwamnati, ciki har da hukumomin gargajiya da masu aikin sa kai a kasar ta Madagaska sun taimaka gayan wajen kawar da cutar ta inna ko kuma Polio.

Masu ruwa da tsaki a kasar sun bukaci da kada a yi watsi da matakan da ake dauka na dakile cutar a sahun gaba da kamfen allurer kafin cutar da ake gudanarwa lokaci zuwa lokaci.

A shekarar 2018,ne  hukumar WHO ta ayyana Madagascar a matsayin kasar da ta kawar da cutar, kafin ta sake fuskantar cutar bayan shekaru biyu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da  Ta’addancinta Kan Iran

Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta jaddada cewa Ta’addancin yahudawan sahayoniyya kan Iran laifi ne na yaki da ya zama wajibi duniya ta yi mata hukunci a kai

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Ismail Baqa’i ya yi kira da a dorawa mahukuntan yahudawan sahayoniyya alhakin munanan laifukan da suka aikata a kan al’ummar Iran, musamman a lokacin da ake ci gaba da kai hare-hare a birnin Tehran fadar mulkin kasar da sauran garuruwan kasar ta Iran.

A wani sakon da ya wallafa a dandalin X a yau Asabar, Baqa’i ya ce, “Harin da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai a asibitoci da kurkukun Evin a ranar 24 ga Yunin wannan shekara ta 2025, wanda ya yi sanadin shahadar fararen hula da ma’aikata da kuma masu shigewa  da yawansu ya kai mutane 79, yana cikin laifukan yaki da kuma keta dokar jin kai ta kasa da kasa.”

Ya yi nuni da cewa, harin ya afku ne a daidai lokacin da iyalan fursunonin ke taruwa domin ziyartar ‘yan uwansu, kuma sun makale a karkashin baraguzan ginin inda suka yi shahada sakamakon harin wuce gona da iri na jirgin saman yakin gwamnatin mamayar Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Al’ummar Iran Ba Zasu Amince Da Ci Gaba Da Zaman Tattaunawa Da Amurka Ba Saboda Fushin Da Suke Ciki Na Kai Musu Hari
  • Kasar Iran Ta Jaddada Wajabcin Hukunta Gwamnatin Mamayar Isra’ila Dangane Da  Ta’addancinta Kan Iran
  • Ma’aikatan MDD Masu Kula Da Ayyukan Makamashin Nukliya Na Kasar Iran Su Fice daga Kasar
  • Kungiyar Hamas Ta Ce Ta Amince Da Tattaunawa Don Kawo Karshen Yaki A Gaza
  • Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita
  • Sin Da Ghana Za Su Karfafa Hadin Gwiwarsu
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gabatar Da Jawabio A Taron Kolin Kungiyar ECO Musamman Kan Harin Da Kasarsa Ta Fuskanta
  • Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
  •  Antonio Guterres Ya Kadu Saboda Mummunan Halin Da Falasdinawan Gaza Suke Ciki
  • Majalisar Jigawa Ta Isa Roni A Ci Gaba Da Rangadin Kananan Hukumomi