Aminiya:
2025-06-20@17:00:27 GMT

NAJERIYA A YAU: Me Ya Sa ‘Yan Gwagwarmaya Ke Shiga Tasku A Najeriya?

Published: 6th, May 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Yin gwagwarmaya ko fafutuka wani abu ne da ke cikin jinin dan Adam, musamman idan yana kokarin ganin an samu sauyi ko cigaba a al’umma.

Sai dai a Najeriya, sau da yawa ana danganta kalmar “gwagwarmaya” da rikici ko sabani da gwamnati.

NAJERIYA A YAU: Abin da ke kai matasan Najeriya ci-rani wasu ƙasashen Afirka DAGA LARABA: Asarar Da Hausawa Ke Tafkawa Sakamakon Bacewar Tatsuniya

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana zai yi nazari ne kan yadda za a yi gwagwarmaya ba tare da an taka doka ba.

Domin Sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwagwarmaya Fafutuka

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja

Shugaban tarayyar Najeriya Bola Tinubu, ya kaddamar da aikin samar da ruwan sha mai tsafta wanda kamfanin CGCOC na kasar Sin ya tallafa wajen gudanar da shi a birnin Abuja, fadar mulkin kasar. Ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa, ta yin aiki tukuru a fannin samar da ababen more rayuwa, da kai tsaye za su inganta rayuwar al’ummun kasar.

Shugaba Tinubu ya bayyana aikin a matsayin muhimmin mataki na tabbatar da al’ummun birnin sun samu ruwa mai tsafta, mai dorewa kuma isasshen a gidaje da hukumomi, da dukkanin sassan birnin. Ya kuma godewa gwamnatin kasar Sin da kamfanin CGCOC, bisa hadin gwiwarsu wajen tabbatar da nasarar aikin.

Yayin da yake nasa tsokaci kuwa a bikin kaddamar da aikin, mukaddashin jakadan Sin a Najeriya Zhang Yi, ya ce aikin na da matukar muhimmanci ga kyautata samar da ruwa a birnin Abuja, kasancewar zai kara yawan ruwan da al’ummar birnin za su iya amfani da shi da rubi uku, wato daga kyubik mita 240,000 zuwa kyubik mita 720,000. Zai kuma baiwa al’ummun birnin har kimanin miliyan uku damar samun isasshen ruwa mai tsafta domin amfanin yau da kullum.

Bugu da kari, karkashin aikin, an horar da ma’aikata ‘yan kasa dabarun samar da ruwa, da fasahohin shimfida bututai, wanda hakan ya samar da guraben ayyukan yi na kai tsaye da wadanda ba na kai tsaye ba har sama da 3,000, matakin da ya ingiza fannin bunkasa kwarewa, da ciyar da tattalin arziki gaba, da ma raya zamantakewar al’ummar birnin na Abuja, kamar dai yadda kamfanin CGC Nigeria, reshen kamfanin CGCOC ya bayyana. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Yadda Tsarin Ilimi Ke Karya Gwiwar ’Yan Najeriya
  • An Kashe ‘Yan Ta’adda 6,260, An Ceto Mutane 5,365 Acikin Shekaru Biyu – Hedikwatar Tsaro 
  • Za a dawo da dukkan Alhazai gida ranar 28 ga Yuni – NAHCON
  • Kotun Amurka ta daure ’yan Najeriya 5 shekaru 159 kan aikata damfara
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Cutar Amosanin Jini Ta Hana Ni Cimma Buri Na
  • Shugaban Najeriya Ya Kaddamar Da Aikin Samar Da Ruwa Da Kamfanin Sin Ya Gudanar A Birnin Abuja
  • Sojoji sun raunata shugaban ISWAP na Najeriya, Albarnawi
  • Litar fetur za ta iya komawa N1,000 a Najeriya saboda yakin Isra’ila-Iran – Masana
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Ƙauyen Kebbi, Sun Kashe Mutane Da Dama
  • DAGA LARABA: Ko Kare Kai Daga Harin ‘Yan Ta’adda Zai Kawo Karshen Matsalar Tsaro?