Amurka Da Haramtacciyar Kasar Isra’ila Sun Taron Dangi Kan Kasar Yemen
Published: 6th, May 2025 GMT
Tawagar jiragen saman yaki da dama ne suka kai munanan hare-hare kan sassa daban-daban na kasar Yemen a jiya Litinin
Kafofin yada labaran kasar Yemen sun rawaito a jiya litinin cewa: Wata tawagar jiragen saman yakin Amurka da haramtacciyar kasar Isra’ila sun kai hare-hare kan yankuna daban-daban na kasar Yemen da suka hada da gundumar Bajil da wasu wurare a gundumar Al Hudaydah da ke yammacin kasar ta Yemen, da kuma gundumar Sinjan da ke birnin San’a.
Ma’aikatar lafiya ta kasar Yemen ta sanar da cewa: Mutane 21 ne suka jikkata sakamakon hare-haren bama-bamai da aka kai kan masana’antar siminti na Bajel da ke gundumar Al Hudaydah.
A nata bangaren, tashar talabijin ta 12 ta haramtacciyar kasar Isra’ila ta nakalto wani jami’in gwamnatin Isra’ila yana cewa: “Sojojin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila sun kaddamar da farmaki kan kasar Yemen a matsayin mayar da martani ga hare-haren makamai masu linzami da Yemen take kai wa a filin jirgin sama na Ben Gurion,” inda ya ce jiragen yakin gwamnatin Isra’ila 30 ne suka shiga cikin kai hare-hare da aka kai Yemen.
Tashar talabijin din ta kara da cewa: “Amurka ta yi ruwan bama-bamai a birnin San’a, sannan haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai hare-hare kan Hodeidah,” tana mai jaddada cewa hare-haren da Isra’ila ke kai wa a Yemen na hadin gwiwa da Amurka ne, kuma Netanyahu ne ke sa ido a kai.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: haramtacciyar kasar Isra ila kasar Yemen
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-haren HKI Akan Syria Da Nufin Rusa Kasar
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran Isma’ila Baka’i ya bayyana cewa; Manufar HKI akan Syria a fili take ba a boye ba.”
Baka’i ya ci gaba da cewa; Manufar HKI ita ce rusa duk wani karfi da Syria take da shi na yaki, da kuma lalata tattalin arzikinta, domin share fagen shimfida iko a kasar da kuma a cikin wannan yankin.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya kuma ci gaba da cewa; matsayin jamhuriyar musulunci ta Iran akan kasar Syria, a fili yake wanda shi ne kare hadin kan wannan kasa da hana ta tarwatsewa da kare daukakarta a matsayinta na kasa mai ‘yanci da kuma al’umma mai tsawo tarihi na ci gaba,sannan kuma mai tasiri a cikin wannan yanki na yammacin Asiya.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen na Iran ya dora alhakin abinda yake faruwa a Syria, akan dukkanin wadanda su ka taka rawa wajen jefa kasar cikin halin da take a yanzu.
Wuraren da HKI ta kai wa hare-hare a daren jiya sun hada da sansanin sojan runduna ta 47 da sojoji Syria dake yankin Humah ta yamma, haka nan kuma rumbun ajiyar makamai na sojan sama a kusa da garub shahdaha, da ya jikkata mutane 4,kamar yadda kamfanin dillancin labaurn “SANA” na kasar ta Syria ya nakalto.
A birnin Damascuss ma sojojin HKI sun kai wasu hare-haren da su ka hada da kusa da fadar shugaban kasa. Kafafen watsa labaru sun ambci shahadar mutum daya, da kuma jikkatar wasu.