OPEC+ Zata Kara Yawan Man Fetur Da Take Haka Da Ganga 411,000 A Cikin Watan Yuli Mai Zuwa
Published: 4th, May 2025 GMT
Kungiyar kasashe masu arzikin man fetur da kuma kawayensu na wajen kungiyar sunce zasu kara yawan man fetur da suke haka da ganga 411,000 a cikin watan Yuli mai zuwa. Kamfanin dillancin labarai na kasar Saudiya ya bayyana cewa kungiyar da kawayenta sun gudanar da taro ta kafar sadarwa ta Bidiyo a ranar 3 ga watan mayu wato jiya inda suka tsaida wannan shawarar.
Labarin ya kara da cewa kungiyar tana son ta maida ganga miliyon 2.2 da suke rage da radin kansu a shekarun bayana a hankali-a hankali. Sannan kungiyar zata ci gaba da gudanr da taro a farkon ko wani wata don sanin yadda kasuwar man take a duniya da kuma yadda zasu ci gaba da kara yawan man da suke haka a ko wani wata har zuwa lokacinda zasu kai mizanin da suka amince da kansa. Don haka taronsu nag aba zai kasance a cikin watan Yuli mai zuwa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Haɗarin tirela ya yi sanadin asarar awaki sama da 100 a Zariya
A daren Juma’a ne dab da wayewar gari wata motar tirela ɗauke da awaki da kaji wadda ta taso daga Gwauron Dutse a Jihar Kano ta yi haɗari.
Motar tirelar wadda take ɗauke da dakon awaki da kuma kwandunan kaji mai yawa a samanta baya ga mutane da ta ɗauko ta yi haɗarin a kusa da kasuwar Ɗan Magaji saman gadar da ke kan hanyar Zariya zuwa Kaduna.
Martani: Har yanzu muna ci gaba da yajin aiki — Ma’aikatan jinya An ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a KebbiAwaki kusan sama da 100 suka mutu da kuma kaji kusan ɗari 500 ne aka ƙeyasta sun mutu.
Sai dai ba a sami asarar rai ko ɗaya ba, sai dai akasarin mutanen da suke motar sun sami raunuka cikinsu har da direban motar, kuma an garzaya da su zuwa Asibitin koyarwa na Jami’ar Ahmadu Bello da ke Shika Zariya don samun kulawar likitoci.
Wasu daga cikin matasan da suka kai ɗauki wurin sun kwashe matattun awakin da kajin inda suka watsa cikin wani kududdufi da ake kiwon kifi a kusa da inda motar ta yi hatsarin dan gudun kada wasu bɓata gari su kwashe dan sayarwa al’umma da mushen matattaun dabbobin.
Wani ganau da ke zaune a wurin da hatsarin ya faru ya ce yana zaton kamar barci ne ya kama direban motar.
A cewar ganau ɗin an tafka asarar sosai na dukiya a hatsarin motar sai dai shugabannin mazauna wurin sun sa ido domin ganin cewa ba a kwashi matattaun dabbobin ayi wani wuri da su ba.
An yi ƙokarin tuntuɓar mai magana da yawu hukumar kula da haɗɗura ta ƙasa reshen Zariya tare da tura masa saƙon kar ta kwana domin jin dalilin faruwar lamarin, amma har zuwa lokacin haɗa rahoton bai ɗauki waya ba.