Wani harin makami mai linzami daga Yemen ya fada filin jirgin saman Ben Gurion na Isra’ila
Published: 4th, May 2025 GMT
Dakarun Yeman ta sanar cewa ta kai hari filin tashi da saukar jiragen sama na Ben Gurion na Falasdinu, a wani mataki na nuna goyon bayansu ga Falasdinawa da ke fama dake fusnkatar mamaya, zalinci da kisan kare dangi daga Isra’ila.
Kakakin rundunar sojin Isra’ila ya ba da rahoton wani sabon hari da makami mai linzami daga Yeman, lamarin da ya tilasta wa mazauna yankin tserewa zuwa matsuguni.
Rundunar ta ce ta kunna na’urar tsaronta ta sama domin tinkarar barazanar, amma ta kasa dakile makamin.
Tun ma kafin sanarwar da sojojin Isra’ila suka fitar, kafofin yada labaran Isra’ila sun ba da rahoton kararrakin gargadin makamai masu linzami a yankuna da dama na tsakiyar Falasdinu da ta mamaye.
Daga baya an sanar da cewa an dakatar da dukkan zirga-zirgar jiragen da ke zuwa filin jirgin Ben Gurion.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jiragen Saman Yakin Sojojin Isra’ila Sun Kai Hare-Haren Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Siriya
Jiragen saman yakin haramtacciyar kasar Isra’ila sun kai hare-hare kan yankunan birnin Damascus fadar mulkin Siriya da kuma yankin yammacin kasar
Majiyoyin cikin gida na kasar Siriya sun bayyana cewa: Jiragen saman yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila sun kai hare-hare ta sama kan sansanonin sojin Siriya bayan da suka yi shawagi a kan garuruwan Hama, Dar’a, Damascus, yankin kan iyakar Siriya da Lebanon da kuma gabar tekun Siriya.
Wadannan su ne fitattun abubuwan da suka faru a lokacin da jiragen saman yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila suka kai wa kasar Siriya hare—haren wuce gona da iri a yammacin ranar Juma’a.
Rahotonni sun kara da cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kaddamar da hare-hare guda biyu kan birnin Al-Tall da ke cikin karkarar Damascus, sannan sun kai wasu hare-hare guda 6 a wajen babban birnin kasar, Damascus, yayin da jiragen yakin ‘yan mamayar suke ci gaba da shawagi a sararin samaniyar Dar’a, As-Suwaida, da Quneitra.