Aikin Gina Tashar Jirgin Ƙasa A Kano Yana Ci Gaba Gadan-gadan
Published: 1st, May 2025 GMT
Faɗin ginin, wanda ya haura sukwaya mita 13,000, ya ƙunshi babban ginin tashar da ababen da ke tattare da shi, kuma zai kasance tashar da ta fi kowace girma a layin dogon da ake kira Kaka Reluwe.
Kaka Reluwe na nufin hanyar dogo daga KAduna zuwa KAno.
Kamfanin CCECC ya ce idan an gama aikin, zai taimaka gaya wajen haɓaka harkokin sufuri kuma ya kawo matuƙar sauƙi ga miliyoyin matafiya a ɓangaren Kano na hanyar jirgin.
Shi dai wannan layin dogo na Kaka Reluwe, hanya ce mai tsawon kilomita 204. Ta tashi daga Kaduna, ta bi ta Zariya, zuwa Kano.
Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ne ya ƙaddamar da ita a ranar 15 ga Yuli, 2021, sannan gwamnatin Bola Ahmed Tinubu tana ci gaba da aikin babu ƙaƙƙautawa don tabbatar da ta kammala ta a kan lokaci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani
Gwamnatin Jihar Jigawa ta horas da Malaman makarantun sakandare kimanin dubu 20 ilimin fasahar sadarwar zamani (digital).
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi ne ya bayyana hakan a lokacin da ya karɓi baƙuncin tawaga daga Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta ƙasa (NITDA) da Cibiyar Zaman Lafiya ƙarƙashin jagorancin Farfesa Hauwa Ibrahim da take Amurka, a ziyarar ban girma da suka kai a gidan gwamnati da ke Dutse.
Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti AllahYa ce: “Mun gabatar da cibiya ta dijital don malamai, don sadarwa da kuma kula da ilmantarwa a matakin farko, mun sanya hannu kan haɗin gwiwa na shekaru biyar tare da NewGlobe don ƙarfafa ƙa’idojin rubutu da ƙididdiga ta amfani da kayan aikin dijital.
“Don haka shirin ku ya yi daidai da gyare-gyaren da muke da su kuma yana ƙara ƙimar ilimi matuƙa.” In ji Namadi.
Gwamna Namadi ya kuma nanata ƙudirin gwamnatin Jigawa na ɗorewar shirin, yana mai cewa, “Ina tabbatar muku: Za mu mallaki wannan shiri, za mu ci gaba da faɗaɗa shi, Kwamishinoninmu na ilimi a matakin farko da kuma na manyan makarantu za su sa ido a kansa.”
Darakta mai riƙon ƙwarya na dijital a Hukumar NITDA, Dokta Ahmed Tambuwal ya bayyana hangen nesa na ƙasa da ke jagorantar shirin.
“Muna nan a matsayin wani ɓangare na Hukumarmu ta NITDA na ci gaba da sadaukar da kai don aiwatar da ajandar Sabuwar Najeriya na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.”
“Babban ginshiƙi na wannan ajandar ita ce rarraba tattalin arzikin Najeriya ta hanyar fasahar dijital.”
Tambuwal ya bayyana cewa, NITDA tana ci gaba wajen cimma buri na kashi 70% na ilimin zamani a shekarar 2027, yana mai jaddada buƙatar haɗin gwiwa don cimma burin.