A daidai lokacin da sabani yake yin tsanani a tsakanin India da Pakistan, bayan wani hari da aka kai a Kashmir da ya yi sanadiyyar mutuwar  mutane 26, ministan tsaron kasar Pakistan Khajah Asif ya ce; matukar India ta keta hurumin kasarsa, to kuwa za ta fuskanci mayar da martani mai tsanani.

Minista Khajah Asif ya kuma gargadi kasar ta India da ta guji keta hurumin kasar Pakistan.

Asif ya kuma bukaci India da ta gudanar da bincike akan harin da aka yi a ranar Talata a yankin Kashmir, kuma ta nesanci yin wani abu wanda zai jefa yankin cikin yakin da ba a san yadda karshensa zai kare ba. Haka nan kuma ya ce; Tushen matsalar tana nan a cikin kasar India,kuma wadanda su ka shirya kai harin suna nan a cikin India, don haka a cikin India ya kamata ta neme su.”

A lokaci daya kuma ministan tsaron na Pakistan ya jadada cewa; Kasarsa ba ta da sha’awar yaki ko kadan, amma idan aka kallafa mata yaki, to martanin da za ta mayar zai zama mafi dacewa kuma  cikin karfi.”

A nashi gefen, ministan harkokin wajen  kasar Pakistan Muhammad Ishaq Dar, ya ce, kasarsa tana sa ido da bibiyar abinda India take yi a kusa, kuma a shirye take ta kare tsaronta da iyakokinta.”

Dar ya kuma fada wa wata  tashar talabijin din cewa; Pakistan kasa ce da take da makaman Nukiliya, tana kuma da dandazon makamai masu linzami masu karfi, kuma India ta kwana da sanin hakan, don haka ta guji keta hurumin kasar Pakistan da tsaronta.”

India ta zargi Pakistan da hannu a harin da aka kai a yankin Kashmir wanda ya yi sanadiyyar mutane 26. Kasar ta India ta kori Jakadan Pakistan daga kasarta, sannan kuma ta kira yi nata jakadan daga Islamabad. Bugu da kari Indiyan ta dakatar da aiki da yarjejeniya akan ruwa a tsakanin kasashen biyu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Pakistan

এছাড়াও পড়ুন:

Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka

Sakatariyar kungiyar kasashen yankin Caribeans  ( Caricom) ta bayyana cewa; kasashen yankin suna son ganin bunkasa alakar kasuwanci da abokansu na nahiyar Afirka.

 Sakatariyar kuniyar ta kasashen Caribbian ta bayyana hakan ne a lokacin jawabin bude taron karawa juna sani a taron kasuwanci da zuba hannun jari a tsakanin yankin da nahiyar Afirka da aka yi a Grenada. Ta kuma kara da cewa:

 Wajibi ne mu bude sabuwar kafar kasuwanci a tsakanin yankunan biyu, kuma ya kamata ace giman kasuwanci a tsakanin bangarorin biyu ya karu da kaso 3% na jumillar kasuwancinmu.”

Kamfanin dillancin labarun “Reuters’ya bayyana cewa wannan matakin na kasashen Caribbean yana nuni da sauyi a huldarsa ta kasunwaci da Amurka da Canada da kuma kasashen turai da su ne abokansu na cinikayya.

  A cikin watan Aprilu ne dai kasar Amurka ta kakabawa dukkanin abokan kasuwancinta kudin fito da sun kai kaso 10%. Bugu da kari Amurkan tana da gagarumin tasiri a cikin harkokin kasuwanci da zuba hannun jari a cikin kasashen yankin na Caribbean.

 Amurka ce babbar abokiyar kasuwancin kasashen yankin Caribbean da take sayen kaso 1/4 na hajar da yankin ke fitarwa da kudin da sun kai dala biliyan 38.8, yayuin da yankin yake sayo kayayyakin da sun kai Dala biliyan 43.4 daga Amurka.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Shugaban Kasar Ivory Coast Ya Bayyana Shirinsa Na Sake Tsayawa Takarar Shugabanci Karo Na Hudu July 30, 2025 Kasashen Iran Da Rasha Sun Tattauna Batun Hadin Gwiwar Kafofin Watsa Labarai A Tsakaninsu July 30, 2025 MDD Zata Aiwatar Da Hanyar Warware Rikicin Falasdinawa Da Yahudawan Sahayoniyya July 30, 2025 Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba July 30, 2025 Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Lod Da Ke Jaffa Da Makami Mai Linzami July 30, 2025 Faransa Ta Bayyana Wuce Gona Da Irin ‘Yan Sahayoniyya Kan Falasdinawa Da Ayyukan Ta’addanci July 30, 2025 Jagora: Iran Ta Bayyana Karfinta Da Jajircewarta A Yakin Kwanaki 12 Ga Duniya July 29, 2025 Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon July 29, 2025 EU Tace Zata Dakatar Da HKI Daga Cibiyar Bincikenta Saboda Gaza July 29, 2025 Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar July 29, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Kasashen Yankin Caribbean Suna Son Bunkasa Alakarsu Ta Kasuwanci Da Nahiyar Afirka
  • Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
  • Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba
  • Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran
  • ’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati
  • Pezeshkiya: Iran A Shirye Take Don Mu’amala Amma Bazata Bar Hakkinta Ba
  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa