A daidai lokacin da sabani yake yin tsanani a tsakanin India da Pakistan, bayan wani hari da aka kai a Kashmir da ya yi sanadiyyar mutuwar  mutane 26, ministan tsaron kasar Pakistan Khajah Asif ya ce; matukar India ta keta hurumin kasarsa, to kuwa za ta fuskanci mayar da martani mai tsanani.

Minista Khajah Asif ya kuma gargadi kasar ta India da ta guji keta hurumin kasar Pakistan.

Asif ya kuma bukaci India da ta gudanar da bincike akan harin da aka yi a ranar Talata a yankin Kashmir, kuma ta nesanci yin wani abu wanda zai jefa yankin cikin yakin da ba a san yadda karshensa zai kare ba. Haka nan kuma ya ce; Tushen matsalar tana nan a cikin kasar India,kuma wadanda su ka shirya kai harin suna nan a cikin India, don haka a cikin India ya kamata ta neme su.”

A lokaci daya kuma ministan tsaron na Pakistan ya jadada cewa; Kasarsa ba ta da sha’awar yaki ko kadan, amma idan aka kallafa mata yaki, to martanin da za ta mayar zai zama mafi dacewa kuma  cikin karfi.”

A nashi gefen, ministan harkokin wajen  kasar Pakistan Muhammad Ishaq Dar, ya ce, kasarsa tana sa ido da bibiyar abinda India take yi a kusa, kuma a shirye take ta kare tsaronta da iyakokinta.”

Dar ya kuma fada wa wata  tashar talabijin din cewa; Pakistan kasa ce da take da makaman Nukiliya, tana kuma da dandazon makamai masu linzami masu karfi, kuma India ta kwana da sanin hakan, don haka ta guji keta hurumin kasar Pakistan da tsaronta.”

India ta zargi Pakistan da hannu a harin da aka kai a yankin Kashmir wanda ya yi sanadiyyar mutane 26. Kasar ta India ta kori Jakadan Pakistan daga kasarta, sannan kuma ta kira yi nata jakadan daga Islamabad. Bugu da kari Indiyan ta dakatar da aiki da yarjejeniya akan ruwa a tsakanin kasashen biyu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Pakistan

এছাড়াও পড়ুন:

Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno

Sanata Ali Ndume, mai wakiltar yankin Borno ta Kudu, ya bayyana cewa hare-haren na ƙara ƙamari a yankin abun takaici ne.

Ya ce ya samu rahoto tsakanin Hawul da Garkida inda aka ce an kashe ’yan sa-kai sama da 10 a ranar Litinin.

A cewarsa, sama da mutane 100 aka kashe cikin wata guda a hare-hare da aka kai Sabon Gari, Izge, Kirawa, Pulka, Damboa, Chibok, Askira Uba da wasu garuruwa da dama.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda ’yan Tifa da baƙin direbobi ke haddasa haɗari a Abuja
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Iran Da Iraki Sun Ce An Kammala Shimfida Layin Dogo Daga Shalamcheh Zuwa Basra
  •  Falasdinawa 40 Sun Yi Shahada A Cikin Sa’oi 24 A Gaza
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jadadda Cewa: Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kan Iran Zai Fuskanci Mayar Da Martani
  • Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan uku
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut