Aminiya:
2025-06-15@06:24:41 GMT

An kori lakcara kan neman lalata da ɗaliba matar aure

Published: 24th, April 2025 GMT

Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) Bauchi ta sallami ɗaya daga cikin malamanta, Dokta Usman Mohammed Aliyu daga jami’ar bisa zargin neman yin lalata da wata ɗaliba matar aure da ke karatun digiri na biyu.

Idan dai ba a manta ba, Kamila Rufa’i Aliyu, ɗalibar Sashen koyon aikin injiniya ce, a shekarar bara ta roƙi mahukuntan Jami’ar ta hannun tsangayarsu da su binciki lamarin.

Yobe na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya mafi zaman lafiya – Buni An kama mata 2 na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace

Ɗalibar ta kuma zargi Dakta Aliyu da yi mata barazanar rashin samun nasarar karatunta idan har ta ƙi amincewa da biyan buƙatarsa.

Malamin da ya samu labarin ƙarar da aka shigar da shi, an shigar da ƙarar a gaban kotu a kan zargin ɓata suna a kan wata ɗaliba, tsangayar da Jami’ar.

Amma Jami’ar a cikin Jaridarta (ATBU Herald) ta Afrilu 22, bugu na Vol. 39 lamba ta 5 ta bayyana cewa majalisar gudanarwa ta jami’ar ta kori Dakta Usman Mohammed Aliyu daga aiki a jami’ar.

Jaridar ta ce: “A zamanta na yau da kullun karo na 96 da aka gudanar a ranar Juma’a, 11 ga Afrilu, 2025, Majalisar ta amince da korar Dakta Aliyu bisa laifin neman yin lalata da ɗalibar.”

Rahoton ya ce korar ta biyo bayan wani rahoton da kwamitin ladabtarwa na manyan ma’aikatan ya yi wanda ya same shi da aikata laifin.

“Sanarwar ta ci gaba da cewa korar ta biyo bayan babi na 3, sashi na 1, (o) na sharuɗɗan manyan ma’aikatan jami’ar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Abubakar Tafawa Balewa ATBU Jami ar

এছাড়াও পড়ুন:

De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City

An sanar da tashin shi daga City kafin karshen kakar wasa ta bana, kuma De Bruyne ya yi bankwana da magoya baya a filin wasa na Etihad bayan wasansa na karshe a gida da suka buga da Bournemouth a watan Mayu, City ta yi kokarin cike gibin da De Bruyne ya bari, yayinda ta dauki yan wasan tsakiya Tijjani Reijnders daga AC Milan da Rayan Cherki daga Lyon.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India
  • De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City