Aminiya:
2025-07-30@15:28:54 GMT

An kori lakcara kan neman lalata da ɗaliba matar aure

Published: 24th, April 2025 GMT

Jami’ar Abubakar Tafawa Balewa (ATBU) Bauchi ta sallami ɗaya daga cikin malamanta, Dokta Usman Mohammed Aliyu daga jami’ar bisa zargin neman yin lalata da wata ɗaliba matar aure da ke karatun digiri na biyu.

Idan dai ba a manta ba, Kamila Rufa’i Aliyu, ɗalibar Sashen koyon aikin injiniya ce, a shekarar bara ta roƙi mahukuntan Jami’ar ta hannun tsangayarsu da su binciki lamarin.

Yobe na ɗaya daga cikin jihohin Najeriya mafi zaman lafiya – Buni An kama mata 2 na ƙoƙarin sayar da ƙananan yara da aka sace

Ɗalibar ta kuma zargi Dakta Aliyu da yi mata barazanar rashin samun nasarar karatunta idan har ta ƙi amincewa da biyan buƙatarsa.

Malamin da ya samu labarin ƙarar da aka shigar da shi, an shigar da ƙarar a gaban kotu a kan zargin ɓata suna a kan wata ɗaliba, tsangayar da Jami’ar.

Amma Jami’ar a cikin Jaridarta (ATBU Herald) ta Afrilu 22, bugu na Vol. 39 lamba ta 5 ta bayyana cewa majalisar gudanarwa ta jami’ar ta kori Dakta Usman Mohammed Aliyu daga aiki a jami’ar.

Jaridar ta ce: “A zamanta na yau da kullun karo na 96 da aka gudanar a ranar Juma’a, 11 ga Afrilu, 2025, Majalisar ta amince da korar Dakta Aliyu bisa laifin neman yin lalata da ɗalibar.”

Rahoton ya ce korar ta biyo bayan wani rahoton da kwamitin ladabtarwa na manyan ma’aikatan ya yi wanda ya same shi da aikata laifin.

“Sanarwar ta ci gaba da cewa korar ta biyo bayan babi na 3, sashi na 1, (o) na sharuɗɗan manyan ma’aikatan jami’ar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Abubakar Tafawa Balewa ATBU Jami ar

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Jami’in Hamas A Gaza; Makiya ‘Yan Sahayoniyya Suna Rufe Gazawar Sojojinsu Da Kisan Kare Dangi

Babban jami’in kungiyar Hamas a Zirin Gaza ya bayyana cewa: Makiya yahudawan sahayoniya suna rufe gazawar sojojinsu da kisan kare dangi

Khalil al-Hayya babban jami’in kungiyar gwagwarmayar Musulunci  ta Hamas a zirin Gaza ya jaddada cewa: Makiya yahudawan sahayoniyya suna rufe gazawar sojojinsu ta hanyar kisan kare dangi da suke aiwatarwa kan fararen hula.

A cikin wani jawabi kai tsaye ta gidan talabijin, Al-Hayya ya bayyana cewa: “Ya ku ‘ya’yan Dakarun Qassam, da na Quds Brigade, da kuma sauran kungiyoyin gwagwarmaya, abin da kuke yi ya kawo cikas ga farmakin da motoci masu sulke na makiya suke yi.

Khalil ya jaddada cewa: Babban hafsan hafsoshin sojin makiya yana rufe gazawar sojojinsa da kisan kare dangi da suke aiwatarwa kan fararen hulan Falasdinawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati
  • ’Yan sa-kai aƙalla 100 da jami’an tsaro 30 sun mutu a bakin aiki a Katsina —Gwamnati
  • An kashe ’yan ta’adda 45 a Neja
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan Almujtaba 121
  • SDP Ta Kori Tsohon Gwamnan Kaduna El-Rufai
  • Babban Jami’in Hamas A Gaza; Makiya ‘Yan Sahayoniyya Suna Rufe Gazawar Sojojinsu Da Kisan Kare Dangi
  • HOTUNA: Yadda Aisha ta koma gidan Buhari na Kaduna
  • Tsohon shugaban jami’ar Kashere ya rasu a Abuja