Shugaban karamar hukumar Birnin Kudu, Alhaji Muhammad Uba Builder, ya sake jaddada kudirinsa na kyakkyawan shugabanci wajen gudanar da harkokin karamar hukumar.

Ya bada  wannan tabbaci ne yayin rabon Naira dubu hamsin hamsin ga mutane 70 da suka amfana da shirin noman alkama da karamar hukumar ta kirkiro.

A cewarsa, mutane 165 ne aka saka cikin shirin, inda matasa 70 daga ciki ‘yan siyasa ne, wadanda a ke da bukatar canza rayuwarsu zuwa hanyoyin neman na kai, duba da cewa siyasa ba sana’a ba ce, illa tsarin shugabanci ne.

Alhaji Muhammad Uba Builder ya ce an samar wa mahalarta shirin da filin noma, tare da gyaran filin, da samar da irin alkama da sauran abubuwan bukata, yayin da suke lura da gonakin har zuwa lokacin girbi.

Ya ce kasancewar wadannan ‘yan siyasa sabbin shiga harkar noma ne yasa ba su samu gagarumar nasara ba, don haka akwai bukatar a kara tallafa musu da jari domin su shiga kananan sana’o’i, yayin da karamar hukumar za ta hada kai da hukumar manoma da makiyaya domin samar musu da kadada daya ta noma ga kowanensu domin su yi noma na damina.

Shugaban ya bukaci jama’a da su yi watsi da jita-jita, su kasance masu juriya, da addu’a ga shugabanni domin su gudanar da aikinsu bisa adalci da gaskiya.

Da suke magana a madadin ‘yan siyasa, Usman Sarki da Bello Ajayi sun sake jaddada kudurinsu na kare mutuncin jihar da shugaban karamar hukumar tare da alkawarin shiga harkokin da za su inganta rayuwarsu ta tattalin arziki.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa karamar hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut

Jiragen yakin HKI sun kai hari a yankin Hangara dake unguwar “Dhahiya” a cikin birnin Beirut. Yankin da jiragen yakin na ‘yan sahayoniya su ka kai wa harin, yana cike da mutane da kuma makarantu biyu.

Jiragen yakin na HKI sun harba makamai masu linzami 3, da hakan ya haddasa tashin gobara.

A sanadiyyar wannan harin, an sami shahidi daya,yayin da wasu da dama su ka jikkata.

A ranar 1 ga watan Aprilu ma dai sojojin HKI sun kai wani harin a unguwar Dhahiya wanda ya yi sanadiyyar shahadar mutane 4 da kuma jikkata wasu da dama.

Tun bayan tsagaita wutar yaki a ranar 27 ga watan Aprilu 2025, HKI ta keta wutar yakin fiye da 2000.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • Gwamna Namadi Ya Nada Aisha Mujaddadi Sabuwar Shugabar Hukumar InvestJigawa
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Hajjin 2025: Jihar Kwara Ta Fara Allurar Rigakafi Ga Maniyyata
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Lebanon:  Isra’ila Ta Kai Hari Akan Unguwar Dhahiya A Birnin Beirut
  • NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”