HausaTv:
2025-05-25@10:49:24 GMT

Hamas ta yi watsi da shirin kwance damara na Isra’ila

Published: 20th, April 2025 GMT

Kungiyar Hamas ta yi watsi da kudirin baya bayan nan na Isra’ila na kwance damarar kungiyoyin gwagwarmayar Falasdinawa domin tsagaita bude wuta a Gaza, tana mai kiran hakan a matsayin wani yunkuri na gurgunta ‘yancin Falasdinu.

Tattaunawar da ake ci gaba da yi tsakanin Isra’ila da Hamas ta tsaya cik, inda Isra’ila ta matsa kaimi kan batun kwance damara, yayin da Hamas ta dage kan hakan a matsayin wani muhimmin hakki na kare Falasdinu.

Mahmoud Mardawi na kungiyar Hamas ya jaddada cewa kwance damarar kungiyoyin gwagwarmayar Falasdinawa abu ne da ba zai yiwu ba.

Ya bayyana kudurin na Isra’ila a matsayin wani dabarun yahudawan sahyoniya da Amurka na kwacewa Falasdinawa karfin kare kansu da kuma tinkarar mamaya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an Sibil Difens sun bude wuta a garin Jos

Mazauna garin Jos sun shiga cikin zullumi bayan da jami’an Hukumar Tsaro ta Sibil Difens (NSCDC) suka yi ta harbe-harbe a ranar Asabar.

Jami’an na Sibil Difens da ke aiki karkashi Hukumar Kula da Ci-gaban Garin Jos (JMDB) sun bude wuta ne a yayin wani samame da suka kai katafare shagon sayar da kayayyaki na S.O Plaza, lamarin da ya haifar da rikici.

Jami’an hukumar sun kuma lakada wa wani matashi mai aiki a plazar duka, lamarin da ya rincabe zuwa tayar da jijiyoyin wuya.

A yayin samamen, jami’an tsaron sun ce sun je ne domin kama wata babbar mota da ta keta dokar  hana manyan motoci shiga garin.

Za mu gina mayankar dabbobi ta Naira biliyan 3 a Gombe —Gwamnati Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 5 a Borno

Amma wani bidiyo da ke yawo ya nuna cewa an ajiye motar ce a cikin harabar plazar kuma ba ta tare hanya ba.

Mazauna garin Jos sun bayyana cewa ba jami’an da ke aiki da JMDB sun yi kaurin suna wajen yin irin haka, inda suke lalata dukiyar jama’a a yayin samamen da suk kaiwa tare da nuna karfin makamai, da ke jefa jama’a cikin firgici.

Mamallakin S.O Plaza, Mista Solomon Okeke, the owner of S.O Plaza, ya bayyana abin a matsayin barna.

Ya kara da cewa ko a watan Agustan bara, wani Manajan Hukumar JMDB, Hart Bankat, ya jagoranci jami’an Sibil Difens zuwa plazar ya sa suka harbe tayoyi shida na wata babbar mota a cikin harabar wurin, wanda ya jawo musu asarar miliyoyin kudade.

Mista Okeke ya bayyana cewa jami’an “sun yi awon gaba da wata babbar mota cike da kaya, kuma sun yi wa wani dan shekara 19 duka suka yayyaga masa kaya, kuma har yanzu ba a san inda yak ba.

“Me ya sa duk lokacin da suka zo sai sun yi ta harbe-harbe suna dukan ma’aikata sun lalata dukiyar jama’a?”

A nasu bangaren, mazauna yakin na Bukuru sun bukaci Gwamna Caleb Mutfwang ya sanya baki tare da taka wa jami’an JMDB burki kan irin yadda suke wuce gona da iri domin a samu zaman lafiya.

Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bakin Janar Manajan JMDB, Akitet Hart Bankat, amma har zuwa lokacin da aka kammala wannan rahoton haka bai samu ba, saboda jami’in bai ba da amsa ga tambayar da aka yi masa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kafafen Watsa Labarun Isra’ila: Kungiyoyin Kasa Da Kasu Sun Ki Shiga Cikin Shirin Isra’ila Da Amurka Na Raba Kayan Agaji
  • Hamas ta yi tir da kiran da dan majalisar dokokin Amurka ya yi na kai farmakin nukiliya a Gaza
  • Rashin abinci mai gina jiki a Gaza ya yi sanadiyar mutuwar mutane 299
  • Jami’an Sibil Difens sun bude wuta a garin Jos
  • Maariv: Tattaunawa A Tsakanin “Isra’ila” Da Kasashen Afirka Ta Yi Nisa Akan Hijirar Mutanen Gaza
  • Hukumar NPA Ta Yi Watsi Da Zargin Cin Hanci Da Rashawa Da Aka Lakaba Mata
  • Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
  • 2027: ’Yan Najeriya sun yi watsi da takarar Tinubu, sun koka kan tsadar rayuwa
  • Jam’iyyar APC A Najeriya Ta Tabbatar Da Tinubu A Matsayin Dan Takarar Shugaban Kasa A Jam’iyyar A Shekara Ta 2027
  •   Ma’ariv: “Isra’ila” Ta Zama Saniyar Ware A Duniya