NAJERIYA A YAU: Sabbin dabarun hana matasa aikata laifi
Published: 19th, April 2025 GMT
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Masu iya magana kan ce, banza ba ta kai zomo kasuwa.
Mai yiwuwa hakan ne ya sa matasan da ake zargi da aikata manyan laifuffuka shiga ofishin ’yan sanda, su kuma fita ba tare da wani ya harare su ba, balle ya kama su.
’Yan sandan dai sun ce wannan wata dabara ce ta yakar aikata manyan laifuka irin su sata da fashi da makami da ƙwacen waya da fyaɗe kai har ma da satar mutane domin karɓar kuɗin fansa a tsakanin matasa.
Ko yaya wannan dabara take aiki?
Wannan ne abin da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Birtaniya ta dage takunkumin da ta kakaba wa wasu manyan jami’an Zimbabwe
Gwamnatin Birtaniya ta sanar da dage takunkumin da ta kakaba wa wasu manyan jami’an gwamnatin Zimbabwe.
Birtaniya ta ce ta yi hakan ne domin kyautata dangantaka tsakanin kasashen biyu.
Ma’aikatar harkokin wajen Birtaniyar ta bayyana cewa za ta dage takunkumin da ke kan mutum hudu da kuma kamfanin kera makamai mallakar gwamnati a Zimbabwe.
Wannan matakin ya zo watanni bayan Tarayyar Turai ita ma ta sassauta nata takunkumin kan Zimbabwe.
Birtaniya ta saka takunkumin ne a lokacin saboda damuwa da abinda ta kira take hakkin dan Adam da aka rika samu a kasar ta Zimbabwe.