Leadership News Hausa:
2025-11-02@17:19:22 GMT

Cutar Da Ke Kassara Gonakin Tumatir Ta Sake Bulla A Jihar Kano

Published: 19th, April 2025 GMT

Cutar Da Ke Kassara Gonakin Tumatir Ta Sake Bulla A Jihar Kano

A cewarsa, hakan ya kuma jawo lalata gonakin na Tumatirin da ke wasu sassan jihar.

Yadakwari ya kara da cewa, hakan ya tilastawa manoman Tumatir da dama a jihar dakatar da nomansa, duba da irin mummunar asarar da suka yi.

Ya ci gaba da cewa, manoman Tumatir da suka fara lura da barkewar cutar ce suka sanar da kungiyar, inda kuma kungiyar ta shigo cikin lamarin ta kuma gano cewa, cutar ce ta sake dawowa gonakin manoman na Tumatir.

A cewarsa, maoman Tumatir a jihar, sun shafe shekaru suna yin asara sakamakon barkewar cutar, wanda hakan ya sanya wa manoman rashin sha’awar ci gaba da noman nasa.

“Mun gano bullar annobar ce a wasu gonakin da aka shuka Tumatir a

Garun Malam, Kura, Bunkure, Bagwai da sauransu”, in ji Yadakwari.

Ya sanar da cewa, duba da ilimin da muke da shi kan cutar, mun yi zargin cewa, annobar ce ta sake dawo ga gonakin na noman Tumatir da ke jihar.

“A bangaren kungiyar, mun dauki matakan da suka dace tare da rubuta wasika zuwa ga ma’aikatar aikin gona ta jihar, domin sanar da su dawowar annobar, inda a yanzu muke ci gaba da jiran amsa daga wurinsu”, a cewar Yadakwari.

Wannan cuta dai, an gano bullarta ne a shekarar 2016, wadda kuma ta jawo lalata gonakin manoma da dama da ke jihar.

Bugu da kari, bayan sake dawowar cutar, an fara fuskantar karancin Tumatir a akasarin kasuwannin da ke jhar, wanda kuma hakan ya haifar da tashin farashinsa zuwa sama da Naira 75.

Kazalika, manomansa da hukumomin gwamnati, sun tashi tsaye wajen yakar wannan cuta, amma sai dai, har yanzu kwalliya ba ta biya kudin sabulu ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai

Gwamnatin Jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin fara amfani da ma’adinan ƙarƙashin ƙasa da Allah SWT ya hore ma ta da nufin haɓaka tattalin arzikinta tare da samarwa al’umma aikin yi.

A yayin ƙaddamar da taron masu ruwa da tsaki na Jihar da aka yi a babban ɗakin taron gidan gwamnatin Jihar da ke Damaturu, Gwamnan Jihar Mai Mala Buni ya ce kamfanin haɓaka ma’adanai ta Yobe Limited ita ce kawai hukumar da aka bai wa izini don gudanar da duk ayyukan bincike da haƙar ma’adinai a faɗin jihar.

Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA

Yana mai cewa, kamfanin haƙar ma’adinai na Yobe a halin yanzu shi ne, ƙashin bayan da zai samarwa Jihar hanyoyin dogaro.

“Jihar Yobe tana da wadataccen albarkatun ma’adinai kamar: Limestone, gypsum, kaolin, granite, Quartz, silica da sauran su duk da haka, tsawon shekaru da yawa, waɗannan ma’adinai sun kasance ba a amfani da su sosai kuma a yanzu lokaci ya yi da za a mayar da waɗannan ma’adinai da aka ɓoye zuwa kadarorin da za su samar da ayyukan yi, samar da wadata da kuma ciyar da ci gaban zamantakewa da tattalin arziki na mutanenmu gaba ɗaya.”

“Manufarmu ita ce tsara wani tsari don ci gaban fannin haƙar ma’adinai a Jihar Yobe ta hanyar da ta dace da manufofin Gwamnatin Tarayya na tabbatar da haɗa kan al’umma, jawo hankalin masu zuba jari masu aminci da kuma tabbatar da alhakin gyara muhalli.

“kuma mun yi imanin cewa haƙar ma’adinai idan aka sarrafa shi yadda ya kamata, zai iya zama babban abin da ke haifar da juriyar tattalin arzikin jiharmu, samar da aikin yi ga matasa da kuma samar da kuɗaɗen shiga.”

“Muna hasashen samar da fannin haƙar ma’adinai wanda zai iya aiki a cikin tsarin dokoki, wanda ke tabbatar da ɗorewar muhalli da fa’idar al’umma; wanda ke haɗaka da haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu waɗanda aka amince da riƙon amana; wanda ke jawo hankalin masu zuba jari na ƙasashen waje.” Cewar Gwamna Buni.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku