Ina gaida Ummi da Baba sai ‘yan uwana yaya Zahra, Yaya Aminu, Yaya Hadiza, Yaya Maimuna, Yaya Rashida, Iman, Amir Da Nurain, sannan kawayena Badi’a Kabir Kwallo, Jamila Sa’ad, Zainab Garba Goro, Yahanasu Imam, Saddika Junaid, Hauwa Uwaisu, da fatan sun yi Juma’a lafiya.
Sako Daga Fatima Zahra Jihar Kano:
Ina gaida Mamana da Abbana da kawaina kamar Rafi’a Kamal, Walida Sadik, Maryam Aliyu, Amina Idris, Khadija Baba, A’isha Fahat, Kursiyya Hamisu, Fiddausi da dai sauransu.
Sako Daga Wasila Adam Nuhu Jihar Kaduna:
Ina gaida Anti A’isha, Anti Ladidi, Anti Balaraba, Uncle Zubair, Uncle Jafar, Uncle Kamalu, Uncle Tajuddeen, Anti Kubra, Anti Sadiya, Uncle Yakub, sai kawayena kamar su; Shaheedah, Yasmin, Zeenat, Meenah, Mahmah, Hanan, Afnan, Fauzy, Ruky, Rumaisa.
Sako Daga Maryam Murtala, Jihar Kano:
Ina gaida Mamy, Maryam Abdullahi, ina gaida kawayena kamar, Khurthum Nasir, Zainab A. Mudi, Halima Saleh, Fatima Kabir Kanwa, Asma’u Muhammad Bello, Muhammad Abdullahi Aminu Mudi, Anwar, Baby Maryam, Anti Fauziyya, Bulun-bulun, Anti Sidiya, Ameerah, Amina, Esha, Anti Safiyya, Mama, Khairiyya, Uncle Hassan, Ibrahim, Uncle Aminu da fatan za su yi juma’a lafiya.
Sako Daga Maryam’s Bakery:
Ina gaida Mum da Dad nawa sannan ina gaida Sisters da brothers dina sai students dina irin su; Deejah, Meerah, Yusra, Nahnah, Zee, Fati, Husna, Priciliar, Kueen Billy, Zainab (first lady), princess Mahmah, Glory, Faith, Maryam Sha’aban, da dai sauran su.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano
Gwamnatin Jihar Kano ta gano ma’aikatanta 240 da ke ƙarɓar albashi sau biyu a duk wata, da wasu 217 da ke amfani da lambar tantance asusun banki (BVN) guda ɗaya.
Wani mai magana da yawun gwamnati, Dakta Sulaiman Wali Sani, ya gaya wa manema labarai a ranar Lahadi cewa an gano wannan badaƙalar ce a yayin da ake tantance tsarin biyan albashin gwamnati.
Dr. Sani ya ce Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi alƙawarin biyan ma’aikata daidai kuma akan lokaci, kuma gano waɗannan matsalolin wani ɓangare ne na gyara al’amura.
Ya ce sun duba bayanan ma’aikata ta hanyar amfani da hotunan yatsa a matakin jiha da ƙananan hukumomi.
“Tsohuwar hanyar biyan mutane tana da matsaloli. Mun gano ma’aikata 240 suna karɓar albashi sau biyu kuma mutane 217 suna amfani da BVN ɗaya, wanda zai iya nufin akwai ma’aikatan bogi ko kuma mutane suna amfani da BVN na wani,” in ji Dakta Sani.
Ya kuma ce ma’aikata 1,335 ba su zo don a tantance su ba a tsawon fiye da watanni shida, wanda ya sa suke tunanin ko waɗannan mutanen da gaske suna aiki da gwamnati.
Alhaji Umar Idi, wanda ya duba biyan kuɗin ƙananan hukumomi, ya ce sun gano sunaye 247 da babu tabbaci a kansu. Waɗannan sun haɗa da mutanen da suka yi ritaya, waɗanda suka mutu, ko kuma waɗanda aka ci gaba da biyan su ba tare da izini ba bayan lokacin barinsu aiki.
“Daga cikin waɗannan ma’aikata 247, takwas ne kawai suka zo don tabbatar da cewa har yanzu suna aiki. Za a goge sauran sunaye 239, wanda zai rage wa gwamnati asarar naira miliyan 27 a duk wata,” in ji shi, yana mai cewa za a mayar da kuɗaɗen da aka samu ga asusun gwamnati.
Dakta Sani ya ce gwamnati ba ta ƙoƙarin hukunta kowa ba, kawai dai tana gyara tsarin ne don ma’aikata na gaske da ’yan fansho su ci gaba da karɓar haƙƙoƙinsu ba tare da wata matsala ko yanka ba bisa ƙa’ida ba.
“Tun lokacin da Gwamna Abba ya fara aiki, ya tabbatar da cewa ana biyan ma’aikatan gwamnati da ’yan fansho a kan lokaci, ba tare da ɓoyayyun cire-cire da aka riƙa yi a baya ba,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa yanzu da suke tsaftace tsarin biyan kuɗi, ma’aikata su yi tsammanin samun biyan kuɗi mafi inganci a gaba.
Gwamnati ta ce za ta ci gaba da magana da duk masu ruwa da tsaki don tabbatar da cewa an magance duk matsalolin kuma jama’a sun sake amincewa da ayyukan gwamnati.