Aminiya:
2025-06-15@01:30:24 GMT

Mutanen da Sanƙarau ta kashe sun kai 151 — NCDC

Published: 7th, April 2025 GMT

Hukumar Yaƙi Da Cututtuka Masu Yaɗuwa a Nijeriya, NCDC ta ce adadin mutanen da suka mutu sakamakon cutar sanƙarau a Nijeriya ya kai 151.

Alƙaluman da hukumar ta fitar sun nuna ƙaruwar waɗanda suka kamu da cutar daga 74 zuwa 156 a jihohin ƙasar 23.

Sojoji biyu da gomman ’yan ta’adda sun rasu a artabu a Borno Zanga-zangar da za mu yi babu gudu babu ja da baya — Take It Back

Jihohin da aka fi samun yawan mace-macen sun haɗa da Kebbi, da Sakkwato da Katsina da Jigawa da Yobe da Bauchi da Gombe da Borno da Kano da Adamawa da kuma Oyo.

NCDC ta ce ta tabbatar da kamuwar wasu mutum 126 daga cikin mutum 1,858 da aka yi zargin suna dauke da cutar a jihohin ƙasar 23.

Wani rahoto da NCDC ta fitar a ranar Lahadi, ta ce jihohin Jigawa, Yobe, Gombe, Katsina, Adamawa, Kebbi da kuma Sakkwato su ne sahun gaba na masu fama da cutar a bayan nan.

Cutar Sanƙarau dai cuta ce da aka fi ɗauka galibi a lokacin zafi.

Wasu mutanen na iya yaɗa cutar ba tare da sun san suna ɗauke da ita ba, akasarin mutanen da ke ɗauke da ita ba su sani ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sanƙarau

এছাড়াও পড়ুন:

An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe

A yayin da ake tsaka da bikin Ranar Dimokradiyya a Najeriya, al’ummar jihar Gombe sun wayi gari da sabuwar dokar takaita zirga-zirgar babura daga ƙarfe 7:00 na yamma zuwa ƙarfe 6:00 na safe a duk faɗin jihar.

Sanarwar da ta fito ne daga hannun Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ’Yan Sanda ta jihar, DSP Buhari Abdullahi, ranar Alhamis, a madadin kwamishinan ’yan sandan jihar Bello Yahaya.

Sanarwar ta ce an kafa dokar ne don rage ayyukan ta’addanci a fadin jihar.

Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato 

Kafa dokar na zuwa ne kwana uku bayan wasu matasa da ba a tantance su wane ne ba suka kashe wani magidanci mai suna Ahmad Aliyu, wanda aka fi sani da Amadi Kasiran, a unguwar Hammadu Kafi da ke Gombe, a daren Lahadi.

Sanarwar ta ƙara da cewa duk wanda aka kama ya karya dokar zai fuskanci hukunci mai tsauri, ciki har da gurfanar da shi a gaban kotu.

Kazalika, sanarwar ta ce dokar ta haramta ɗaukar mutum fiye da ɗaya a kan babur domin rage matsalar rashin tsaro a jihar.

“Dokar hana hawa babur da goyon biyu ta fara aiki ne daga yau, Alhamis, ranar bikin Dimokradiyya, har sai wani lokaci da ba a kayyade ba,” in ji Kakakin ’yan sandan.

Rundunar ’yan sandan ta ce an ɗauki wannan mataki ne don magance matsalar bata-gari na ‘’yan kalare’ da sauran ayyukan ta’addanci.

A lokacin da wakilinmu ya kai ziyara kwaryar birnin Gombe, filin wasa na Pantami ya kasance a rufe ba tare da alamar wani biki ba.

Sai dai ya gane wa idanunsa cewa an jibge jami’an tsaro a sassa daban-daban, ciki har da ’yan sanda, jami’an tsaro na farin kaya (DSS), da kuma ’yan banga.

Wannan sabuwar doka ta ja hankalin mutane da dama a jihar, musamman mazauna yankunan da aka fi samun matsalar tsaro.

Sai dai wasu na gani za ta kara jefa jihar cikin kuncin talauci sakamakon rufe shaguna da kasuwanni da wuri saboda rashin abun hawa wanda dama can baburan aka fi hawa saboda tsadar rayuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Darussan Hadisin Aikin Hajjin Manzon Allah S.A.W (2)
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • An hana hawa babur da daddare a fadin jihar Gombe
  • An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato
  • An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato