Leadership News Hausa:
2025-11-03@09:46:05 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18]

Published: 26th, March 2025 GMT

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [18]

1. Gibɗa a cikin Addini:
Wannan ya ƙunshi yin gasa a ibada kamar sallah, ko azumi, ko karatun Alƙur’ani, da sadaka, ko mutum ya so ya zama hamshaƙin mai kuɗi da zai rinƙa taimaka wa addini da bayin Allah. Ko kuma mutum ya nemi ya zama malami ko jagora a addini don ya koyar da mutane.

2. Gibɗa a cikin Duniya:
Wannan shi ne mutum ya so samun ilimi irin na wasu don ya amfanar da kansa da al’umma.

Ko kuma son ya zama attajiri ko ɗan kasuwa ko mai wata sana’a da zai rinƙa ba wa mutane horo saboda ya ga wani yana yi shi ma ya so ya ƙware ya taimaka domin samun lada a wurin Allah. Haka nan son samun shugabanci mai kyau domin jagorantar al’umma bisa gaskiya.

Manzon Allah (SAW) ya nuna irin wannanhassadarba laifi ba ce, inda ya ce: “Babu hassada sai a cikin abubuwa biyu: mutumin da Allah Ya ba shi ilimi, sai ya yi aiki da shi yana koyar da mutane, da kuma mutumin da Allah Ya ba shi dukiya, sai ya kashe ta a cikin hanyar da ta dace.” Bukhari da Muslim ne suka ruwaito.

Bambanci Tsakanin Hassada da Gibɗa:

Idan mutum ya ga wani yana da ilimi, sannan ya so ya zama kamar shi ba tare da yana son ilimin wancan ya gushe ba, to wannan ita ce gibɗa. Idan kuma mutum yana jin haushin wani saboda Allah Ya ba shi wata ni’ima, yana kuma son ni’imar ta gushe daga gare shi, to wannan ita ce hassada wacce aka haramta.

Illon Mutum Ya Zama Maras Gibɗa:
Idan mutum bai da hali na gibɗa, to hakan zai haifar masa da:

• Rashin ƙwazo da son ci gaba a rayuwa.
• Rashin yin koyi da na-gari a al’umma.
• Watsi da neman ilimi da kwarewa a sana’a ko addini.
• Rashin gasa a ayyukan ibada, wanda zai iya sa mutum ya ja baya a addini.

Yadda Mutum Zai Zama Mai Gibɗa:

Idan mutjm yana son ya sami ta gari, to dole ne ya zamanto ya:

• Nemi arzƙi ta hanyar halal da nagartaccen ilimi mai amfani.
• Aiki tuƙuru don samun ci gaba, ba tare da cutar da wani ba.
• Yin addu’a don Allah Ya ba shi irin ni’ima da wasu ke da ita.
• Kauracewa hassada da kiyayya a zuciya.
Kallon wasu a matsayin abin koyi, ba makiya ba.

Allah Ya datar da mu. Amin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Abu Razina Nuhu Ubale Paki Ramadan Allah Ya ba shi

এছাড়াও পড়ুন:

Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar

Gwamna Inuwa ya kuma jaddada bukatar bin ka’idojin kariya a harkokin sufurin ruwa, inda ya yi kira ga shugabannin kananan hukumomi, da shugabannin al’umma, da direbobin kwale-kwale da hukumomin da ke da ruwa da tsaki da sauran wadanda suka dace su kara kaimi wajen ganin ana kiyaye duk ka’idojin kariya don magance sake afkuwar ibtila’in a nan gaba.

Ya umurci Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta Jiha (SEMA) da Majalisar. Karamar Hukumar Nafada su bayar da duk wani tallafin da ya dace ga iyalan da abin ya shafa tare da hada hannu da hukumomin da abin ya shafa don inganta tsaro da wayar da kan al’ummomin da ke yankunan kogi.

Gwamna Inuwa Yahaya ya yi addu’a yana mai cewa “A madadin gwamnati da al’ummar Jihar Gombe, ina mika sakon ta’aziyyarmu ga iyalan mamatan tare da addu’ar Allah ya jikansu da rahama ya gafarta musu kurakuransu, ya kuma saka musu da Aljannar Firdaus”.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025 Manyan Labarai Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi October 31, 2025 Manyan Labarai Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi
  • Allah Ya yi wa Malam Nata’ala rasuwa
  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Maganin Nankarwa (3)
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • Yan Nijeriya Na Ɗanɗana Kuɗarsu Kan Jinkirta Cire Tallafin Mai – Sarki Sanusi