Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren Gwamnati
Published: 25th, March 2025 GMT
Shugaban riƙo na Jihar Ribas, Ibok-Ete Ibas (mai ritaya), ya sanar da naɗin Farfesa Ibibia Lucky Worika a matsayin sabon Sakataren Gwamnatin Jihar Ribas.
Wata sanarwa da ta fito daga Fadar Gwamnatin da ke birnin Fatakwal a wannan Talatar, ta ce naɗin ya biyo bayan nazari kan ƙwarewar Farfesan da gogewarsa a fannoni daban-daban.
Naɗin sabon Sakataren Gwamnatin na zuwa ne a daidai lokacin da Ibas ya amince da murabus ɗin Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, George Nwaeke, yana mai gode masa bisa gudunmawar da ya bayar a lokacinsa.
Ibas ya ce naɗin Farfesa Worika ya yi daidai da manufofin sa na amfani da ƙwararru daga jihar Ribas domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.
A halin yanzu, an naɗa Iyingi Brown, Babbar Sakatare a Ofishin Shugaban Ma’aikata, a matsayin mai riƙon muƙamin har zuwa lokacin da za a naɗa sabon shugaba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Ribas Sakataren gwamnati Vice Admiral Ibok ete Ibas
এছাড়াও পড়ুন:
Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja
Gwamnan Jihar Neja, Umar Mohammed Bago, ya janyo ce-ce-ku-ce a fadin Najeriya bayan da ya sake jaddada cewa duk wani malamin addini da ke shirin yin wa’azi dole ne ya gabatar da rubutaccen wa’azinsa domin tantancewa kafin ya gabatar da shi ga jama’a.
A cewar gwamnatin jihar, wannan mataki na da nufin daƙile kalaman ƙiyayya, tsattsauran ra’ayi da barazanar tsaro da ke tasowa daga wa’azin da ba a tantance ba.
Da yake jawabi a shirin Politics on Sunday na gidan talabijin na TVC, Gwamna Bago ya musanta zargin cewa dokar ta hana wa’azi gaba ɗaya, yana mai cewa matakin na da nufin tabbatar da zaman lafiya da hana tayar da fitina.
Gwamnan ya ce:
“Ban hana wa’azi ba. Duk wanda zai yi wa’azi a ranar Juma’a, ya kawo rubutaccen wa’azinsa domin tantancewa. Wannan ba sabon abu ba ne. A Saudiyya ma haka ake yi. Ba za a bar malami ya yi wa’azi da ke cin mutuncin jama’a ko gwamnati ba, yana mai cewa ba da damar yin wa’azi ba yana nufin a yi amfani da damar wajen tayar da hankali.”
Gwamnan ya bayyana cewa gwamnati na aiki kafaɗa da kafaɗa da hukumomin tsaro kamar DSS, ’yan Sanda, Sibil Difens da sojoji domin sa ido kan wa’azin da ka iya tayar da hankali.
Matakin ya fara jawo ce-ce-ku-ce ne bayan da Darakta Janar na Hukumar Kula da Harkokin Addini ta Jihar Neja, Umar Farooq, ya sanar da cewa duk wani malami dole ne ya nemi lasisin wa’azi cikin watanni biyu ko ya fuskanci hukunci.
“Abin da ake bukata shi ne su zo ofishinmu, su cike fom, sannan su fuskanci kwamitin tantancewa kafin su fara wa’azi,” in ji Farooq.
Wannan sanarwa ta haifar da martani iri-iri daga shugabannin addini da ƙungiyoyin fararen hula, inda da dama ke nuna fargabar cewa dokar za ta iya zama hanyar danne ’yancin faɗin albarkacin baki.
Babban Limamin Jami’ar Fasaha ta Minna, Sheikh Bashir Yankuzo, ya bayyana ra’ayi mai sassauci, yana mai cewa duk da cewa gwamnati na da haƙƙin daƙile kalaman ƙiyayya, ba za ta hana wa’azi na gaskiya ba.
Sheikh Yankuzo ya ce:
“Wa’azi umarni ne daga Allah, kuma gwamnati ba ta biya kowa albashi don yin wa’azi. Amma idan akwai masu tayar da hankali ko amfani da kalaman batanci, to gwamnati na da ikon dakile hakan don tabbatar da zaman lafiya.”
Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) reshen Jihar Neja ta bakin Sakataren ta, Raphael Opawoye, ta ce ba a sanar da su hukuncin ba.
“CAN ba ta da masaniya kan dokar. Za mu fitar da sanarwa idan an sanar da mu a hukumance,” in ji Opawoye.
Sai dai wani malamin addinin Musulunci, Ustaz Uthman Siraja, ya soki dokar kwata-kwata, yana mai cewa ta take ‘yancin addini da ibada.
Ya bayyana cewa:
“Hana wa’azi cin zarafin ’yancin addini ne. Mafi alheri shi ne gwamnati ta gayyato malamin da ya tayar da hankali ta hukunta shi, ba wai a tantance wa’azi gaba ɗaya ba.”
Gwamna Bago ya kare dokar da cewa matakin tsaro ne na rigakafi, musamman ganin tarihin jihar na fuskantar hare-haren ’yan bindiga, rikicin addini da tsattsauran ra’ayi.
Yayin da wa’adin cike fom da samun lasisi ke ƙara matsowa, idanu sun karkata zuwa Jihar Neja don ganin ko dokar za ta kawo zaman lafiya ko kuma ta ƙara dagula al’amura tsakanin gwamnati da al’ummar addini.