Aminiya:
2025-06-15@18:00:01 GMT

Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren Gwamnati

Published: 25th, March 2025 GMT

Shugaban riƙo na Jihar Ribas, Ibok-Ete Ibas (mai ritaya), ya sanar da naɗin Farfesa Ibibia Lucky Worika a matsayin sabon Sakataren Gwamnatin Jihar Ribas.

Wata sanarwa da ta fito daga Fadar Gwamnatin da ke birnin Fatakwal a wannan Talatar, ta ce naɗin ya biyo bayan nazari kan ƙwarewar Farfesan da gogewarsa a fannoni daban-daban.

Za mu ɗauko hayar sojojin ƙetare domin horas da dakarun Nijeriya — Badaru Gaskiyar abin da ake faɗa kan ’yan fim — Samira Sani

Naɗin sabon Sakataren Gwamnatin na zuwa ne a daidai lokacin da Ibas ya amince da murabus ɗin Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, George Nwaeke, yana mai gode masa bisa gudunmawar da ya bayar a lokacinsa.

Ibas ya ce naɗin Farfesa Worika ya yi daidai da manufofin sa na amfani da ƙwararru daga jihar Ribas domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

A halin yanzu, an naɗa Iyingi Brown, Babbar Sakatare a Ofishin Shugaban Ma’aikata, a matsayin mai riƙon muƙamin har zuwa lokacin da za a naɗa sabon shugaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Ribas Sakataren gwamnati Vice Admiral Ibok ete Ibas

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai

Gwamnatin Tarayya ta bayyana aniyar ɗaukar matakai masu tsauri kan duk wanda aka samu da hannu a harkar fasa bututun mai da satar ɗanyen mai a yankin Niger Delta. Daraktan Tsaron Makamashi a Ofishin Mai baiwa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro (ONSA), Hon. Ojukaye Flag-Amachree, ne ya bayyana haka yayin wani taron masu ruwa da tsaki da kamfanin Pipeline Infrastructure Nigeria Limited (PINL) ya shirya a birnin Fatakwal.

A cewarsa, tuni sama da mutum 100 da ake zargi da hannu a wannan haramtacciyar harka an gurfanar da su a gaban kotu. Ya ce duk wanda aka kama, komai muƙaminsa, za a hukunta shi bisa doka. Ya kuma roki shugabannin al’umma da su ja kunnen matasa da yara kada su shiga lalata bututun mai.

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai Ƴansanda Sun Damke Ango Da Abokansa Bayan Mutuwar Amarya A Jigawa

Ya ce: “Muna roƙonku da ku yi magana da ‘yan uwanmu. Muna sanin mutanen da ke wannan harka, ku shawarce su su daina. Yanzu abubuwa ba kamar da ba ne. Fiye da mutum 100 tuni an hukunta su. Ko kai Soja ne, ko Janar ne, muddin aka same ka da laifi, za ka fuskanci hukunci.”

A nasa ɓangaren, Jami’in hulɗa da jama’a na PINL, Tarilah Alamieseigha, ya bayyana cewa kamfanin ya amince da bayar da tallafin karatu har guda 646 da wasu ƙarin shirye-shirye ga al’ummomi 215 da ke kusa da bututun Trans Niger Pipeline (TNP). Ya yaba da haɗin kan da ke tsakanin kamfanin da al’ummomi, wanda ya taimaka wajen bunƙasa samar da mai a ƙasa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Cece-Kuce Ya Barke Bayan Ganduje Da Shugaban APC Na Arewa Maso Gabas Sun Nemi A Sauya Shettima A 2027
  • Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Bayyana Sabon Salon Mayar Da Martani Kan Isra’ila
  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025