Aminiya:
2025-08-01@14:34:04 GMT

Kantoman Ribas ya naɗa sabon Sakataren Gwamnati

Published: 25th, March 2025 GMT

Shugaban riƙo na Jihar Ribas, Ibok-Ete Ibas (mai ritaya), ya sanar da naɗin Farfesa Ibibia Lucky Worika a matsayin sabon Sakataren Gwamnatin Jihar Ribas.

Wata sanarwa da ta fito daga Fadar Gwamnatin da ke birnin Fatakwal a wannan Talatar, ta ce naɗin ya biyo bayan nazari kan ƙwarewar Farfesan da gogewarsa a fannoni daban-daban.

Za mu ɗauko hayar sojojin ƙetare domin horas da dakarun Nijeriya — Badaru Gaskiyar abin da ake faɗa kan ’yan fim — Samira Sani

Naɗin sabon Sakataren Gwamnatin na zuwa ne a daidai lokacin da Ibas ya amince da murabus ɗin Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, George Nwaeke, yana mai gode masa bisa gudunmawar da ya bayar a lokacinsa.

Ibas ya ce naɗin Farfesa Worika ya yi daidai da manufofin sa na amfani da ƙwararru daga jihar Ribas domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

A halin yanzu, an naɗa Iyingi Brown, Babbar Sakatare a Ofishin Shugaban Ma’aikata, a matsayin mai riƙon muƙamin har zuwa lokacin da za a naɗa sabon shugaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Jihar Ribas Sakataren gwamnati Vice Admiral Ibok ete Ibas

এছাড়াও পড়ুন:

APC Zamfara Ta Taya Sabon Sarkin Katsinar Gusau Murna

Jam’iyyar APC reshen Jihar Zamfara ta taya sabon mai martaba Sarkin Katsinar Gusau, Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello, murnar hawansa karagar mulki a matsayin Sarkin Katsinan Gusau na 16.

 

Jam’iyyar a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun sakataren yada labaranta, Yusuf Idris Gusau, ta bayyana sabon sarkin a matsayin mai tarihi da kuma nadin sarautar Allah, wanda ya zo ne jim kadan bayan rasuwar mahaifinsa, marigayi sarki, Alhaji Ibrahim Bello.

 

Sanarwar ta nuna cewa Alhaji Abdulkadir kyawawan halaye na gaskiya, kwazonsa, sadaukarwa, biyayya ga mahaifinsa da ya rasu, da kuma mutunta al’umma ta kowane hali, sun nuna shi ne wanda ya cancanta.

 

A cewar sanarwar, wannan shi ne karo na farko a tarihin masarautar da wani dan da ya haifa kai tsaye ya gaji mahaifinsa, wanda jam’iyyar ta ce hakan yana nuna yardar Allah da kuma ci gaba da gadon adalci na marigayi sarki.

 

Jam’iyyar APC ta bukaci sabon sarkin da ya kiyaye dabi’u da abubuwan gado na mahaifinsa da kakanni, musamman na fitaccen malamin addinin musulunci kuma shugaba, Sambo Dan-Ashafa.

 

Jam’iyyar ta yi addu’ar Allah ya yi masa jagora, ya kare shi, da kuma hikimar Sarki don ya jagoranci al’umma zuwa ga zaman lafiya da wadata.

 

Har ila yau, ta ba da tabbacin ci gaba da goyon bayanta da shirye-shiryenta na neman shawara, jagoranci, da albarka daga sabon sarki.

 

Daga karshe sanarwar da sakon fatan alheri ga mai martaba sarki da daukacin masarautar Gusau.

 

 

REL/AMINU DALHATU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi?
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Tinubu ya naɗa sabon shugaban hukumar kashe gobara ta ƙasa
  • Shugabannin Arewa Sun Tattauna Sabon Hanyar Ci Gaba – Minista Uba Maigari Ya Yaba
  • APC Zamfara Ta Taya Sabon Sarkin Katsinar Gusau Murna
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Gwamnatin Zamfara ta amince da naɗin sabon Sarkin Katsinan Gusau