Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-16@04:20:24 GMT

Liverpool na farautar Kerkez, Real Madrid na son Konate

Published: 6th, March 2025 GMT

Liverpool na farautar Kerkez, Real Madrid na son Konate

Liverpool na farautar ɗan wasan Bournemouth mai shekara 21 daga Hungary Milos Kerkez kan fam miliyan 40. (Telegraph – subscription required)

 

West Ham na kokarin ganin ta saye ɗan wasan tsakiya a Ingila, Angel Gomes mai shekara 24 daga Lille a sabuwar kaka. (Guardian)

 

Manchester United na tunanin ɗauko mai tsaron raga a Burnley, James Trafford mai shekara 22 ko kuma Joan Garcia mai shekara 23 daga Sifaniya, domin maye gurbin Andre Onana mai shekara 28 na Kamaru.

(Teamtalk)

 

Real Madrid na son ɗan wasan Liverpool mai shekara 25 daga Faransa, Ibrahima Konate. (Mail – subscription required)

 

Real ta kuma nuna matsuwa kan ɗan wasan Bournemouth mai shekara 19 daga Sifaniya, Dean Huijsen, wanda cikin yarjejeniyarsa ake iya biyan fam miliyan 50 domin sayensa ga wata ƙungiya. (Talksport)

 

Barcelona na duba yiwuwar mallake ɗan wasan Newcastle mai shekara 27 daga Brazil, Bruno Guimaraes, wanda ƙungiyoyin Arsenal da Manchester City ke zawarci. (CaughtOffside)

 

Ɗan wasan tsakiya a Bayern Munich da Jamus, Joshua Kimmich mai shekara 30 na son zuwa Arsenal, yayinda ita ma Paris St-Germain ke nuna zawarcinta. (Bild – in German)

 

Ɗan wasan Manchester United da Brazil, Antony mai shekara 25, ya nuna sha’awar cigaba da zama a Real Betis idan yarjejeniyar zaman aronsa ta kawo karshe a ƙungiyar ta La Liga club. (Canal Sur, via Mail)

 

Liverpool ta kasance ƙungiya ta baya-bayanan da ke zawarcin ɗan wasan RB Leipzig, Benjamin Sesko mai shekara 21 daga Slovenia wanda burinsa ya je Landan, sannan Arsenal da Chelsea na bibbiyarsa. (TBR Football)

 

Tottenham na iya rabuwa da ɗan wasan Mali, Yves Bissouma mai shekara 28 a wannan kaka, yayinda take kokarin sake garambawul a tawagarta. (Football Insider)

 

West Ham ta tuntubi ɗan wasan Roma mai shekara 27 da Ingila,Tammy Abraham, da yanzu haka ke zaman aro a AC Milan. (Teamtalk)

 

Newcastle na duba yiwuwar saye ɗan wasan Fiorentina, mai shekara 25 daga Italiya, Moise Kean. (GiveMesport), external

 

Everton za ta bada damar sake daidatawa kan ɗan wasan Brazil, Richarlison mai shekara 27 daga Tottenham. (TBR Football)

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Wasanni mai shekara

এছাড়াও পড়ুন:

Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi

Tsohon Gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi, ya ce har yanzu Najeriya ba ta kai matsayin cin ribar cikakkiyar dimokuraɗiyya ba, duk da cewa an dawo mulkin farar hula shekaru 26 da suka gabata.

Yayin wata tattaunawarsa da gidan talabijin na Channels, domin bikin Ranar Dimokuraɗiyya, Fayemi ya bayyana cewa duk da cewa ana gudanar da zaɓe a kai a kai a ƙasar, har yanzu an rasa muhimman abubuwan da suka kamata su kasance a tsarin dimokuraɗiyya na gaskiya.

Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna

“Bai kamata mu rikita gudanar da zaɓe da aiwatar da dimokuraɗiyya ba,” in ji shi.

“Abin da muka samu a 1999 shi ne ’yancin zaɓar shugabanni, amma hakan kawai ɓangare ne guda ɗaya.

“Abin da muke da shi mulkin farar hula ne, ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba.”

Ya ce an samu ci gaba a ƙarƙashin gwamnatoci daban-daban tun daga baya, amma har yanzu Najeriya na buƙatar ƙarfafa al’adar dimokuraɗiyya da sauye-sauyen da suka dace.

Fayemi ya kuma tuna da lokacin da ya kasance ɗaya daga cikin masu fafutukar dimokuraɗiyya a zamanin mulkin soja, musamman a lokacin marigayi Janar Sani Abacha.

Ya bayyana yadda suka gudanar da shirye-shirye a wani gidan rediyo a aka ɓoye, don ƙalubalantar gwamnatin soji.

“Ba wai rashin tsoro ba ne, mun san hatsarin da ke tattare da lamarin, amma mun yi imani da abin da muke yi,” in ji shi.

“Na taɓa ɗaukar na’urar watsa shirye-shiryen rediyon Kudirat a cikin jirgin Air France da ya sauka a Legas lokacin da fafutukar ta yi zafi. Wannan kaɗai na iya jefa ni cikin hatsari.”

Ya ce waɗanda suka mutu a lokacin ba don sakaci suka rasa rayukansu ba, sai don sun gaskata ƙudurinsu na ganin an samu ’yanci.

Fayemi ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu bisa karrama wasu daga cikin waɗanda suka fafata wajen dawo da dimokuraɗiyya.

Sai dai ya nuna damuwa cewa wasu da dama da suka taka muhimmiyar rawa a bayan fage ba a karrama su ba.

“Mutane da dama sun sa rayuwarsu cikin hatsari. Su ma sun cancanci a yaba musu.

“Ba daidai ba ne a girmama waɗanda ake gani a manta da waɗanda suka bayar da gudunmawarsu a bayan fage.”

Maganganun Fayemi sun haifar da zazzafar muhawara kan yadda Najeriya ke da buƙatar ci gaba kafin a kira ta da ƙasar da ke da cikakkiyar dimokuraɗiyya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta kai sabbin hare-hare birnin Tel Aviv da Haifa
  • Dan Asalin Tudun Loess
  • An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • Wakilin Sin: Matakin Amurka Game Da Harajin Kwastam Bai Yi La’akari Da Rarar Cinikayyar Hidimomi Ba
  • Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Jagoran Juyin Musulunci Na Iran Ya Nada Sabbin Kwamandojin Soja Da Dakarun Kare Juyin Musulunci
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje