Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-03@07:57:22 GMT

Liverpool na farautar Kerkez, Real Madrid na son Konate

Published: 6th, March 2025 GMT

Liverpool na farautar Kerkez, Real Madrid na son Konate

Liverpool na farautar ɗan wasan Bournemouth mai shekara 21 daga Hungary Milos Kerkez kan fam miliyan 40. (Telegraph – subscription required)

 

West Ham na kokarin ganin ta saye ɗan wasan tsakiya a Ingila, Angel Gomes mai shekara 24 daga Lille a sabuwar kaka. (Guardian)

 

Manchester United na tunanin ɗauko mai tsaron raga a Burnley, James Trafford mai shekara 22 ko kuma Joan Garcia mai shekara 23 daga Sifaniya, domin maye gurbin Andre Onana mai shekara 28 na Kamaru.

(Teamtalk)

 

Real Madrid na son ɗan wasan Liverpool mai shekara 25 daga Faransa, Ibrahima Konate. (Mail – subscription required)

 

Real ta kuma nuna matsuwa kan ɗan wasan Bournemouth mai shekara 19 daga Sifaniya, Dean Huijsen, wanda cikin yarjejeniyarsa ake iya biyan fam miliyan 50 domin sayensa ga wata ƙungiya. (Talksport)

 

Barcelona na duba yiwuwar mallake ɗan wasan Newcastle mai shekara 27 daga Brazil, Bruno Guimaraes, wanda ƙungiyoyin Arsenal da Manchester City ke zawarci. (CaughtOffside)

 

Ɗan wasan tsakiya a Bayern Munich da Jamus, Joshua Kimmich mai shekara 30 na son zuwa Arsenal, yayinda ita ma Paris St-Germain ke nuna zawarcinta. (Bild – in German)

 

Ɗan wasan Manchester United da Brazil, Antony mai shekara 25, ya nuna sha’awar cigaba da zama a Real Betis idan yarjejeniyar zaman aronsa ta kawo karshe a ƙungiyar ta La Liga club. (Canal Sur, via Mail)

 

Liverpool ta kasance ƙungiya ta baya-bayanan da ke zawarcin ɗan wasan RB Leipzig, Benjamin Sesko mai shekara 21 daga Slovenia wanda burinsa ya je Landan, sannan Arsenal da Chelsea na bibbiyarsa. (TBR Football)

 

Tottenham na iya rabuwa da ɗan wasan Mali, Yves Bissouma mai shekara 28 a wannan kaka, yayinda take kokarin sake garambawul a tawagarta. (Football Insider)

 

West Ham ta tuntubi ɗan wasan Roma mai shekara 27 da Ingila,Tammy Abraham, da yanzu haka ke zaman aro a AC Milan. (Teamtalk)

 

Newcastle na duba yiwuwar saye ɗan wasan Fiorentina, mai shekara 25 daga Italiya, Moise Kean. (GiveMesport), external

 

Everton za ta bada damar sake daidatawa kan ɗan wasan Brazil, Richarlison mai shekara 27 daga Tottenham. (TBR Football)

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Wasanni mai shekara

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi

Wasu ’yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da fasinjoji a cikin wasu motocin bas Toyota guda biyu a titin Itobe zuwa Ajegwu-Anyigba a Ƙaramar hukumar Ofu ta jihar Kogi.

An samu rahoton cewa, lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 5 na asubahi a tsakanin ƙauyukan Ojiwo’-Ajengo da Mamereboh da ke kan babbar hanyar.

Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa

An ce masu garkuwa da mutanen sun yi amfani da wata tirela da aka kama wajen tare hanyar bayan shingen binciken jami’an tsaro, da ke kusa da wurin da lamarin ya faru.

Shedun gani da ido sun ce ɗaya daga cikin motocin bas ɗin mai lamba KG: KPA 622LG na kan hanyarta zuwa Abuja, tare da fasinjoji daga wata tashar mota a unguwar Ankpa da ke yankin Kogi ta Gabas.

Har yanzu ba a iya gano adadin fasinjojin da aka yi garkuwa da su ba zuwa yanzu, sai dai mun iya tabbatar da cewa ɗaya daga cikin motocin na ɗauke da fasinjoji ne daga yankin Ankpa, kamar yadda aka gano wasu takardu da wasu kayayyaki a wurin da lamarin ya faru suka bayyana.

“Motocin bas ɗin guda biyu suna kan hanyar Abuja ne a lokacin da suka ci karo da shingayen ’yan bindiga a safiyar ranar Alhamis. Dukkanin fasinjojin, ciki har da direban motocin bas ɗin biyu an yi awon gaba da su cikin daji,” in ji Unubi Ademu, wani mazaunin Achigili, a ƙauyen da ke maƙwabta.

Al’ummar yankin sun ƙara da cewa, jami’an tsaro da suka haɗa da sojoji da mafarauta da kuma ’yan banga suna ƙoƙarin magance lamarin.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan Jihar Kogi (PPRO), CSP William Aya bai amsa kira da saƙo ba lokacin da aka tuntuɓe shi har zuwa lokacin tattatara wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA