Leadership News Hausa:
2025-07-31@22:13:41 GMT

Za Mu Doke Atletico Madrid Har Gida, Hansi Flick

Published: 1st, March 2025 GMT

Za Mu Doke Atletico Madrid Har Gida, Hansi Flick

Kociyan kungiyar kwallon kafa ta Barcelona, Hansi Flick, ya bayyana cewa kungiyarsa za ta je har gidan Atletico Madrid ta doke ta a wasan kusa da na karshe na gasar cin kofin Coppa Del Rey, bayan da Barcelona da Atletico Madrid suka tashi 4-4 a wasan farko zagayen daf da karshe a Copa del Rey ranar Talata a filin wasa na Estadi Olimpic Lluis Companys.

Minti daya da fara wasan Atletico Madrid ta fara cin kwallo ta hannun Julian Albarez, sannan Griezmann ya kara ta biyu a minti na biyar Tsakani amma daga baya Barcelona ta zare daya ta hannun Pedri a minti na 19, sannan Cubarsi ya farke ta biyu minti uku Tsakani sannan kafin hutu Barcelona ta kara ta uku ta hannun Martinez, haka suka je zagayen farko Barcelona na cin 3-2.

Noman Dabino: Jigawa Ta Yi Hadaka Da Saudiyya Yawan ’Yan Kasashen Waje Da Suka Shigo Kasar Sin Ba Tare Da Biza Ba A Bara Ya Ninku

Bayan da suka koma zagaye na biyu ne, sai Barcelona ta ci ta hudu a karawar ta hannun Lewandowski kai kace an tashi da Atletico Madrid a wasan amma daga baya kungiyar da Diego Simeone ke jan ragama ta zare kwallo ta uku ta hannun Llorente daga baya ta zare ta hudu ta hannun Sørloth dab da za a tashi daga wasan wanda yaja hankalin ‘yan kallo a duniya.

Wannan shi ne karo na biyu da suka kece raini a tsakaninsu a bana, bayan da Atletico ta je ta doke Barcelona a La Liga ranar 21 ga watan Disamba kuma a ranar Laraba 4 ga watan Afirilu, Atletico za ta karbi bakuncin wasa na biyu a daf da karshe a Copa del Rey. Barcelona ce ta daya a kan teburin La Liga da maki 54, iri daya da na Real Madrid ta biyu da kuma Atletico mai maki 53 ta ukun teburin babbar gasar tamaula ta Sifaniya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Barcelona

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya karɓi baƙuncin ɗan Majalisar Tarayya mai wakiltar ƙananan hukumomin Kiru da Bebeji na Jihar Kano, Abdulmumin Jibrin Kofa.

Aminiya ta ruwaito cewa Kofa, wanda makusanci ne ga jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, kuma ɗaya daga cikin jiga-jigai a jam’iyyar NNPP, ya ziyarci shugaban ƙasar ne a yau Laraba.

Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya Tattalin arzikin Nijeriya zai ci gaba da bunƙasa har zuwa baɗi — IMF

Har yanzu dai babu wasu bayanai dangane da abin da suka tattauna, amma ziyarar wadda hadimai daga ɓangarorin biyu suka riƙa yaɗawa na ci gaba da ɗaukar hankalin jama’a.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matsayar Bai Daya Da Sin Da Amurka Suka Cimma Ta Fuskar Haraji Na Da Babbar Ma’ana
  • Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah
  • Kare Ya Ciji Tsohon Ɗan Wasan Barcelona A Mazakuta
  • Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure
  • Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon
  • Wakilin Gidan Talabijin Na Al-Alam Ya Bayyana Yadda Shi Da Iyalansa Suka Rayu Kwanaki Biyu Babu Abinci A Gaza