Aminiya:
2025-06-15@20:04:36 GMT

Buhari ya koma Kaduna da zama bayan shafe shekara 2 a Daura

Published: 27th, February 2025 GMT

Tsohon Shugaban Ƙasa, Muhammadu Buhari, ya koma gidansa da ke Jihar Kaduna da zama, bayan shafe shekara biyu a Daura, tun bayan barinsa mulki a watan Mayun 2023.

Buhari, ya zaɓi yin rayuwa mai sauƙi bayan kammala wa’adin mulkinsa ba tare da shiga harkokin siyasa ba.

Gwamnatin Kano ta nemi Tinubu ya kori Aminu Bayero daga fadar Nassarawa Malaman Jami’ar Sakkwato sun tsunduma yajin aiki

Ya samu rakiyar Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, da manyan jami’an gwamnati zuwa Kaduna.

Daga cikin tawagar da suka yi masa rakiya akwai Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, mataimakan gwamnan Jihar Katsina, Tsohon Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, wasu tsofaffin ministoci, da wasu daga cikin hadimansa.

A lokacin da yake barin Katsina, jama’a da yawa sun taru don yi wa Buhari fatan alheri.

Daga cikin manyan da suka yi masa rakiya akwai Malam Mamman Daura, Musa Halilu (Dujiman Adamawa), da Bashir Ahmad.

Komawa Kaduna na nufin wani sabon mataki a rayuwarsa bayan shafe shekara biyu a Daura.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Buhari Daura Rakiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran

Ya umurci jami’an tsaro su gaggauta kai dauki ba tare da bata lokaci ba don tabbatar da an gurfanar da masu laifin a gaban kuliya, yana mai jaddada cewa za a hukunta duk wanda aka samu dauke da muggan makamai ko kuma aka samu yana da hannu wajen aikata laifuka.

“Ga iyalai da ‘yan uwa da masoyan marigayi Ahmed, ina mika sakon ta’aziyyata, da na gwamnati da al’ummar Jihar Gombe, kuma muna jimami tare da ku, ina ba ku tabbacin za a yi adalci.

“Ina kuma kira ga jami’an tsaro su kara kaimi wajen tattara bayanan sirri da kuma sintiri kan tituna, musamman a wuraren da ke fuskantar irin wadannan laifuka. Jama’armu sun cancanci tafiya cikin walwala ba tare da tsoro ko barazana ga rayuka da dukiyoyinsu ba.

“Muna ci gaba da jajircewa wajen kare kowane rai da kuma tabbatar da cewa zaman lafiya da tsaro sun ci gaba da wanzuwa a wannar jiharmu.”

Ya yi kira ga al’umma su tallafa wa jami’an tsaro ta hanyar ba su bayanai masu muhimmanci kan lokaci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
  • HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina
  • Martanin sojojin Iran ga Isra’ila zai zama mafi muni idan aka ci gaba da kai hari (Pezeshkian)
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray