HausaTv:
2025-05-01@04:35:00 GMT

MDD Ta Yi Gargadi Akan Tsanantar Yunwa A Kasar Sudan

Published: 27th, February 2025 GMT

A jiya Laraba ne dai Hukumar da take kula da harkokin jin kai dake karkashin MDD  ( OCHA) ta bayyana cewa; Kusan shekaru biyu na yakin da ake yi a Sudan ya kara tsananta, kuma a halin yanzu yunwa wani abu ne da ya zama dahir ana ganinta a kasa a Sudan.

Babbar daraktan  gudanar da ayyukan hukumar agajin ta MDD Edem Wosornu ta fadawa kwamitin tsaron MDD cewa; Da akwai mutane miliyan 12 da aka tarwasta daga gidajensu, daga cikinsu da akwai wasu miliyan 3.

4 da su ka tsallaka iyaka. Haka nan kuma fiye da rabin mutanen kasar Miliyan 24.6 suna fama da matsananciyar yunwa.”

Haka nan kuma ta kara da cewa; Tsarin kiwon lafiya na kasar ya durkushe baki daya, da akwai miliyoyin kananan yara da su ka daina karatu, wasu kuma an ci zarafinsu.”

Bugu da kari, saboda fadan da ake ci gaba da yi, an dakatar da kai kayan agaji zuwa sansanin ‘yan hijira mafi girma na Zamzam, alhali suna da bukatuwa da agajin.

A ranar Litinin da ta gabata ne dai kungiyar likitoci ba tare da iyaka ba        ( Médecins Sans Frontières )  ta nuna rashin jin dadinta da yadda rashin tsaro ya tilasata ta dakata da ayyukanta a sansanin Zamzam.

Jakadan Sudan A MDD Al-Harith Idriss ya ce, kasarsa a shirye take ta samar da yanayin da zai bayar da damar ci gaba da gudanar da ayyukan agaji a kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu

Shugaban  kungiyar hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’imKasim ya bayyana cewa, kungiyarsa tare da Sojojin kasar da kuma mutanen kasar ne zasu tabbatar da ci gaban kasar Lebanon a wannan halin da ake ciki.

Tashar talabijin ta Al-Mayadeen ta nakalto sheikh Na’im kasim yana fadar haka a wani jawabin da ya gabatar a jiya Litinin, jawabinda kafafen yada labarai da damaa suka watsa kai tsaye.

Sheikh Qasim kasar Lebanon zata ci gaba da zama mai karfi idan gwamnatin kasar ta dakatar da hare-haren da HKI take  ci gaba da kawowa a kan kasar, da kwato dukkan yankunan kasar da aka mamaye, har’ila yau da kuma ci gaba da hadin kai tsakanin masu gwagwarmaya, sojoji da kuma mutanen kasar.

Shugaban kungiyar ya jadda bukatar sake gina wuraren da HKI ta rusa a yankunan daban daban a kasar, ya ce gwamnatin kasar ta yi alkawalin zata sake gina wuraren da HKI ta rusa a yakin da hizbullah a baya-bayan nan.

Kuma ya ce rashin yin haka nuna bambanci ne a tsakanin mutanen kasar. Ya ce dangane da wadanda aka rusa gidajensu kungiyar ta bada kudaden haya ga 50,755 , sannan ta gyura wasu 332 da aka lalata, wanda duk aikin gwamnati ne ta yi hakan. Don haka akwai bukatar gwamnati ta aikata wajibin da ya hau kanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Jaridar The Guardian Mafi Yawan ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Ne A Gidan Yarin Kasar Girka
  • HKI Tana Amfani Yunwa A Matsayin Makamin Yaki  A Kan Falasdinawa A Gaza
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Shugaban Kasar Yana Maraba Da Masu Zuba Hannun Jari A Kasarsa Daga Kasashen Waje
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Takht Ravanji: Iran Ba Za Ta Taba Yin Tattaunawa Akan Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium Ba
  • Uganda Ta Sanar Da Kawo Karshen Ebola Da Ta Barke A Kasar