Aminiya:
2025-09-18@01:15:32 GMT

Abba ya ba da umarnin bincike kan rage wa ma’aikatan Kano albashi

Published: 27th, February 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan ƙorafe-ƙorafen datse wa ma’aikatan jihar albashi.

Hakazalika ya ce a yi bincike kan rashin biyan wasu ma’aikatan albashinsu.

Zulum ya rage adadin tallafin rabon abinci da kashi 90 a Borno An shiga ruɗani bayan Obasa ya koma majalisar Legas da ’yan sanda

Ya bayyana lamarin a matsayin cin zarafin ma’aikata da tauye musu haƙƙi.

Rahotanni sun nuna cewa wasu ma’aikatan sun shafe watanni ba tare da karɓar cikakken albashinsu ba.

Gwamna Abba ya sha alwashin gano waɗanda ke da hannu a lamarin tare da hukunta su.

“Wannan gwamnati ba za ta amince da zaluntar ma’aikata ba.

“Duk wanda aka samu da hannu a wannan laifi zai fuskanci hukunci,” in ji shi.

Don shawo kan matsalar, gwamnan ya kafa kwamitin bincike mai mutum bakwai ƙarƙashin jagorancin Abdulkadir Abdussalam, Kwamishinan Kula da Ci Gaban Karkara wanda kuma shi ne tsohon Akanta-Janar na Jihar.

Akwai ƙwararru a harkar kuɗi da manyan jami’an gwamnati a cikin kwamitin, waɗanda za su duba takardun albashi daga watan Oktoban 2024 zuwa Fabrairun 2025.

Ayyukan kwamitin sun haɗa da gano ma’aikatan da abin ya shafa, tantance asarar kuɗi da kuma bayar da shawarwari kan yadda za a magance matsalar gaba ɗaya.

Gwamnan ya bai wa kwamitin wa’adin kwana bakwai don kammala bincikensa da kuma miƙa rahoton.

Gwamna Abba ya tabbatar wa ma’aikatan jihar cewa gwamnatinsa za ta tabbatar da adalci da kuma biyan albashi a kan lokaci a nan gaba.

Ya gargaɗi duk wanda aka samu da laifin yin almundahana da albashin ma’aikata cewa ba za a kyale shi ba.

Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Alhaji Umar Faruk Ibrahim ne, ya ƙaddamar da kwamitin a madadin gwamnan.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ta shiga tsakani don sasanta rikicin da ya ɓarke tsakanin Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH) da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Shiyyar Kano (KEDCO).

Rikicin ya samo asali ne daga katse wutar lantarki da asibitin ya zargi KEDCO da yi, inda ya ce hakan ya kawo cikas ga ayyukan lafiya masu muhimmanci a asibitin, ciki har da zargin mutuwar marasa lafiya.

Sasantawar da Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya jagoranta ta biyo bayan zarge-zargen cewa katsewar wutar ta haddasa mutuwar wasu marasa lafiya da ke kan na’urar taimakon numfashi a asibitin.

Sai dai KEDCO ya musanta zargin a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin, yana mai cewa asibitin na kokarin bata sunansa ne kawai.

A cewar mai magana da yawun ‘yan sanda na Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, an gudanar da taron sasancin ne a hedikwatar ‘yan sandan Kano da ke Bompai, inda aka zauna da Shugaban asibitin, Farfesa Abdulrahman Abba Sheshe, da Shugaban KEDCO, Abubakar Shuaibu Jimeta.

Taron ya mayar da hankali ne kan warware tankiyar da kuma dawo da wutar lantarki ga asibitin, wanda ke ya fuskanci matsaloli sakamakon katse wutar.

Sanarwar ta ce, “Bangarorin biyu sun nuna godiya ga matakin gaggawa da ‘yan sanda suka dauka. KEDCO ya amince da dawo da wutar lantarki nan take, alamar cewa rikicin ya zo karshe.”

Kiyawa ya kara da cewa, “Rundunar ‘Yan Sanda ta jaddada kudirinta na kare rayuka da dukiyoyi, tare da tabbatar da ci gaba da aiki ba tare da tangarda ba a bangaren kiwon lafiya.”

Sanarwar ta kuma ce kwamishinan ‘yan sanda ya yaba wa AKTH da KEDCO bisa hadin kai, tare da alkawarin ci gaba da goyon baya don tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA
  • KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano