Abba ya ba da umarnin bincike kan rage wa ma’aikatan Kano albashi
Published: 27th, February 2025 GMT
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan ƙorafe-ƙorafen datse wa ma’aikatan jihar albashi.
Hakazalika ya ce a yi bincike kan rashin biyan wasu ma’aikatan albashinsu.
Zulum ya rage adadin tallafin rabon abinci da kashi 90 a Borno An shiga ruɗani bayan Obasa ya koma majalisar Legas da ’yan sandaYa bayyana lamarin a matsayin cin zarafin ma’aikata da tauye musu haƙƙi.
Rahotanni sun nuna cewa wasu ma’aikatan sun shafe watanni ba tare da karɓar cikakken albashinsu ba.
Gwamna Abba ya sha alwashin gano waɗanda ke da hannu a lamarin tare da hukunta su.
“Wannan gwamnati ba za ta amince da zaluntar ma’aikata ba.
“Duk wanda aka samu da hannu a wannan laifi zai fuskanci hukunci,” in ji shi.
Don shawo kan matsalar, gwamnan ya kafa kwamitin bincike mai mutum bakwai ƙarƙashin jagorancin Abdulkadir Abdussalam, Kwamishinan Kula da Ci Gaban Karkara wanda kuma shi ne tsohon Akanta-Janar na Jihar.
Akwai ƙwararru a harkar kuɗi da manyan jami’an gwamnati a cikin kwamitin, waɗanda za su duba takardun albashi daga watan Oktoban 2024 zuwa Fabrairun 2025.
Ayyukan kwamitin sun haɗa da gano ma’aikatan da abin ya shafa, tantance asarar kuɗi da kuma bayar da shawarwari kan yadda za a magance matsalar gaba ɗaya.
Gwamnan ya bai wa kwamitin wa’adin kwana bakwai don kammala bincikensa da kuma miƙa rahoton.
Gwamna Abba ya tabbatar wa ma’aikatan jihar cewa gwamnatinsa za ta tabbatar da adalci da kuma biyan albashi a kan lokaci a nan gaba.
Ya gargaɗi duk wanda aka samu da laifin yin almundahana da albashin ma’aikata cewa ba za a kyale shi ba.
Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Alhaji Umar Faruk Ibrahim ne, ya ƙaddamar da kwamitin a madadin gwamnan.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamitin Neman Sabuwar Karamar Hukumar Kanya Babba Ya Gabatar Da Takardar Bukatarsa Ga Majalisar Dattawa
Kwamitin neman sabuwar Karamar Hukumar Kanya Babba daga Karamar Hukumar Babura ta Jihar Jigawa, ya gabatar da takardar bukatarsa ga kwamitin Majalisar Dattawa mai kula da kirkiro jihohi da kananan hukumomi a zaman da aka yi a jihar Kano.
A yayin mika takardar, Shugaban kwamitin kuma Hakimin Kanya Babba, Makaman Ringim, Malam Mohammed Ibrahim ya bayyana cewar wannan yunkuri ya bi duk sharuddan da kundin tsarin mulki ya shimfida don kafa sabuwar karamar hukuma.
Makaman na Ringim ya kara da cewar, daukacin al’ummar yankin Kanya Babba, ciki da wajen mazabar na matukar goyon bayan hakan domin bunkasa ci gaban tattalin arziki da al’umma a yankin.
Da yake karbar takardar, Shugaban kwamitin Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibril, ya nuna jin dadin sa da jajircewar mutanen Kanya Babba wajen mika takardar.
Barau Jibrin, ya kuma tabbatar musu kwamitinsa zai yi adalci da gaskiya a aikin da aka dora musa.
Wakilinmu ya bamu rahoton cewar, taron mika bukatar ya samu halartar mataimakin Gwamnan jihar Jigawa, Injiniya Aminu Usman da Sanatan Jigawa ta Arewa maso Yamma, Alhaji Babangida Husaini da dan majalisar jiha mai wakiltar mazabar Kanya, Alhaji Ibrahim Hashim Kanya da shugaban Karamar Hukumar Babura, Alhaji Hamisu Muhammad Garu da mai bawa gwamna shawara kan harkokin bada aiyukan kwangila Usman Haladu Isa da Alhaji Salisu Muazu Kanya da hakimai da Dagatai da ‘yan siyasa da kuma sauran masu ruwa da tsaki da dimbin masoya.
Usman Mohammed Zaria