Aminiya:
2025-11-03@09:26:31 GMT

Abba ya ba da umarnin bincike kan rage wa ma’aikatan Kano albashi

Published: 27th, February 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayar da umarnin gudanar da bincike kan ƙorafe-ƙorafen datse wa ma’aikatan jihar albashi.

Hakazalika ya ce a yi bincike kan rashin biyan wasu ma’aikatan albashinsu.

Zulum ya rage adadin tallafin rabon abinci da kashi 90 a Borno An shiga ruɗani bayan Obasa ya koma majalisar Legas da ’yan sanda

Ya bayyana lamarin a matsayin cin zarafin ma’aikata da tauye musu haƙƙi.

Rahotanni sun nuna cewa wasu ma’aikatan sun shafe watanni ba tare da karɓar cikakken albashinsu ba.

Gwamna Abba ya sha alwashin gano waɗanda ke da hannu a lamarin tare da hukunta su.

“Wannan gwamnati ba za ta amince da zaluntar ma’aikata ba.

“Duk wanda aka samu da hannu a wannan laifi zai fuskanci hukunci,” in ji shi.

Don shawo kan matsalar, gwamnan ya kafa kwamitin bincike mai mutum bakwai ƙarƙashin jagorancin Abdulkadir Abdussalam, Kwamishinan Kula da Ci Gaban Karkara wanda kuma shi ne tsohon Akanta-Janar na Jihar.

Akwai ƙwararru a harkar kuɗi da manyan jami’an gwamnati a cikin kwamitin, waɗanda za su duba takardun albashi daga watan Oktoban 2024 zuwa Fabrairun 2025.

Ayyukan kwamitin sun haɗa da gano ma’aikatan da abin ya shafa, tantance asarar kuɗi da kuma bayar da shawarwari kan yadda za a magance matsalar gaba ɗaya.

Gwamnan ya bai wa kwamitin wa’adin kwana bakwai don kammala bincikensa da kuma miƙa rahoton.

Gwamna Abba ya tabbatar wa ma’aikatan jihar cewa gwamnatinsa za ta tabbatar da adalci da kuma biyan albashi a kan lokaci a nan gaba.

Ya gargaɗi duk wanda aka samu da laifin yin almundahana da albashin ma’aikata cewa ba za a kyale shi ba.

Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Alhaji Umar Faruk Ibrahim ne, ya ƙaddamar da kwamitin a madadin gwamnan.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?

Shi ma wasan da ta yi nasara a kan kungiyar Sifaniya a daf da za a tashi ta ci kwallon a gasar Zakarun Turai da na Newcastle United a Premier League. Tun daga nan alamomi suka fara bayyana cewar akwai tarin matsaloli a Liberpool, wadda kowanne wasa kwallo ke shiga ragarta in ban da wanda ta yi nasara a kan Arsenal 1-0 a Premier League cikin Agusta da wanda ta ci Burnley 1-0 a cikin watan Satumba a Premier League.

Sababbnin ‘Yanwasan da Liberpool ta saya a kakar banamages Giorgi Mamardashbili daga Balencia Jeremie Frimpong daga Bayern Leberkusen, Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen,

Milos Kerkez daga Bournemouth, Hugo Ekitike daga Eintracht Frankfurt, Aledander Isak daga Newcastle United, Armin Pecsi daga Puskas Akademia. Giobanni Leoni daga Parma Freddie Woodman daga Preston North, Will Wright daga Salford.

Wasu daga cikin matsalolin Liberpool A Yanzu

Matsalar masu buga mata tsakiya Liberpool ta samu sauye-sauye da yawa a fannin masu taka mata wasa daga tsakiya, bayan da wasu daga ciki suka bar kungiyar, ya dace a ce ta hada

fitattun da za ta fuskanci kakar bana.

Liberpool ta dauki Florian Wirtz daga Bayern Leberkusen, amma har yanzu dan wasan bai nuna kansa ba, inda yake ta shan suka daga magoya bayan da suke ganin kwalliya ba za ta biya kudin sabulu ba.

Raunin ‘yanwasa da ke jinya

Raunin da wasu ‘yanwasan Liberpool suka ji sun taka rawar gani da kungiyar Liberpool ke kasa kokari a kakar nan. Daga ciki mai tsaron baya, Giobanni Leoni ya ji rauni a wasansa na farko a kungiyar, wanda ake cewa yana doguwar jinya. Mai tsaron raga Alisson Becker ya ji rauni a lokacin gasar zakarun turai wanda ake cewar zai yi jinya har karshen watan Oktoba, watakila ya wuce hakan.

Bayan Liberpool na yoyo

A kakar bara bayan Liberpool ya yi yoyo, duk da cewar kungiyar ce ta lashe kofin, amma dai an samu matsaloli da yawa a bayan. Kungiyoyi da dama sun amfana da kurakuren Liberpool a bara daga ciki har da Nottingham Forest da Brighton da kuma Brentford.

Wasu lokutan da zarar Liberpool ta kai kora sai kaga wagegen gibi tsakanin masu tsare baya da ‘yan tsakiya. Haka kuma tun kafin fara kakar bana, Liberpool ta buga wasannin atisaye, kuma tun a lokacin gurbin masu tsare baya ya nuna matasalar da kungiyar za ta iya fuskanta da fara

kakar nan.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025? November 1, 2025 Wasanni Barcelona Na Shirin Ɗauko Victor Osimhen Na Galatasaray October 30, 2025 Wasanni Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi October 28, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kano Ta Amince Da Naira Biliyan 8.2 Don Ayyukan ilimi, Samar Da Ruwa, Da Makamashi
  • Kano Pillars Ta Koma Matsayi Na 20 Bayan Shan Kashi A Hannun Enyimba
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda