Shugaban Hafsan Sojan Sama Na Najeriya Ya Zama Shugaban Kungiyar Sojojin Sama Na Afrika
Published: 27th, February 2025 GMT
Shugaban Hafsan Sojan Sama, Air Marshal Hasan Abubakar ya zama Shugaban Kungiyar Sojojin Sama na Afrika-AAAF.
Da yake jawabi a wajen taron shugabannin sojojin saman Afrika da aka gudanar a kasar Zambiya, Air Marshal Hasan Abubakar, ya jadadda bukatar samar da hanyoyin warware kalubalen tsaro da kasashen Afirka ke fuskanta.
A cikin wata sanarwa da daraktan hulda da jama’a da yada labarai na NAF, Air Vice Marshal Olusola Akinboyewa, ya fitar, hafsan hafsoshin ya bayyana muhimmancin hadin gwiwa tsakanin shiyya da dabarun hadin gwiwa wajen karfafa karfin jiragen na Afrika da kuma magance barazanar da ake fuskanta.
Ya jaddada cewa, inganta hadin gwiwa tsakanin sojojin saman Afrika na da matukar muhimmanci wajen tunkarar kalubalen tsaro da ke kunno kai kamar ta’addanci, tada kayar baya da kuma laifuffukan kasa da kasa.
Air Marshal Hasan Abubakar ya lura da cewa taron na nuni ne da jajircewa wajen tabbatar da tsaro, kwanciyar hankali da wadata a Afirka.
Ya yi kira da a sabunta alkawari daga dukkan mambobin, yana mai jaddada cewa hadin kai na da matukar muhimmanci wajen cimma manufofin kungiyar.
A cewar sanarwar, kungiyar ta AAAF, kungiya ce mai zaman kanta da ba ta siyasa ba, da ta himmatu wajen inganta karfin samar da kariyarar sararin samaniyar Africa da hadin gwiwa tsakanin kasashen Afirka.
PR/Usman Sani.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Nijeriya hadin gwiwa
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas: HKI Da Amurka Sun Janye Daga Tattaunawa Ne Don Sake Damarar Yaki
Shugaban kungiyar Hamass ya bayyana cewa HKI da gwamnatin kasar Amurka sun janye daga tattaunawa tsakaninsu da kungiyar ne don sake komawa yaki har zuwa lokacinda zasu shafe falasdinawa a gaza.
Tashar talabijin nta Presstv a nan Tehran ya nakalto Kkalilul Hayya, yana fadar haka a wani jawabin da aka watsa a tashoshin talabijin nay au Litinin.
Alhayya ya bayyana cewa akwai ci gaba a tattaunawar tsagaiuta wuta tsakanin kungiyar da HKI da kuma Amurka, amma janyewar HKI da kuma Amurka a wannan tattaunawar wata dasisa ce don ci gaba da kissan kiyashi a gaza.
Ya ce: masu shiga tsakanin sun tabbatar da cewa akwai ci gaba a tattaunawar da ake yi a doha, sai dai sun janye ne don samun lokacinda da zasu gaggauta kissan Falasdinawa a Gaza, don cimma mummunan manufofinsu a gaza.
Dangane da rabon kayakin agaji wanda HKI da Amurska suka shira kuma Alhayya ya yi allawadai da shi ya kuma kara da cewa cibiyoyin bada agajin tarko ne na kara kissan Falasdinawa a Gaza.
Ya kara da cewa shirin GHF na Amurka da kuma HKI shiri ne na kissan karin Falasdinawa bayan sun sanyasu cikin yunwa na kimani watanni biyu kafin su fara rabon abinda suke kira agaji.