Aminiya:
2025-09-17@23:26:13 GMT

Buhari da El-Rufai ba su halarci babban taron APC ba

Published: 26th, February 2025 GMT

Jam’iyyar APC mai mulki, ta gudanar da babban taronta na ƙasa a Abuja, wanda ya samu halartar manyan jiga-jigan jam’iyyar daban-daban.

Duk da kasancewar Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu da mataimakinsa, Kashim Shettima a waje taron, wasu manyan shugabannin jam’iyyar ba su halarci taron ba.

Ƙungiya ta raba wa marayu da mabuƙata kayan makaranta a Kano Shugabannin APC sun gana gabanin babban taron jam’iyyar na ƙasa

Daga cikin waɗanda ba su halarci taron ba akwai tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, tsohon gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufai, da tsohon gwamnan Ribas, Rotimi Amaechi.

Dalilin Rashin Halartar Buhari

Dangane da dalilin da ya sa Buhari bai samu halartar taron ba, tsohon mai magana da yawunsa, Malam Garba Shehu, ya bayyana cewa tsohon shugaban bai samu katin gayyata a kan lokaci ba.

“Taron masu ruwa da tsaki ne, wanda ya kamata Buhari ya halarta. Amma an aike masa da gayyatar taron ne a ranar Litinin, sai dai bai samu wasiƙar ba sai ranar Talata da rana.

“A wannan lokacin, ba zai iya barin Daura ya tafi Abuja don halarta ba, ko da kuwa yana da jirginsa na musamman.”

Duk da hakan, Garba Shehu ya jaddada cewa Buhari har yanzu cikakken ɗan jam’iyyar APC ne kuma zuciyarsa tana tare da ita.

Dalilin Rashin Halartar El-Rufai da Amaechi

Babu cikakken bayani game da dalilin da ya sa Malam Nasir El-Rufai bai halarci taron ba.

Sai dai a baya, tsohon gwamnan na Kaduna ya sha bayyana rashin jin daɗinsa game da jagorancin jam’iyyar, inda zargi cewa ta sauka daga aƙidar da aka kafa ta.

Duk da haka, ya nanata cewar har yanzu shi cikakken ɗan jam’iyyar.

Shi ma Rotimi Amaechi bai bayyana dalilin rashin halartarsa ba.

A kwanakin baya dai, tsohon gwamnan na Ribas ya daina yawan magana a fili.

A wata hira da ya yi da BBC, ya ce: “Idan akwai abu guda ɗaya da na koya daga Shugaba Buhari, shi ne rage yawan surutu.

“Domin ya taba fada min cewa ‘Amaechi, ba don abinci kawai aka yi ciki ba.’“

Manyan Jiga-Jigan da Suka Halarci Taron

Daga cikin gwamnonin da suka halarci taron akwai na jihohin Edo, Benuwe, Ondo, Ekiti, Kaduna, Jigawa, Nasarawa, Yobe, Nejs, Legas, Kogi, Ogun, da Imo.

Mataimakin gwamnan Ebonyi da wasu tsofaffin gwamnoni daga Kogi, Kebbi, Neja, Zamfara, da Filato su ma sun halarci taron.

Duk da rashin halartar wasu daga cikin manyan jiga-jigan jam’iyyar, babban taron ya gudana kamar yadda aka tsara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Buhari jam iyya taro tsohon gwamnan halarci taron babban taron

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin Jiang Bin, ya ce a baya bayan nan babban jirgin ruwan dakon jiragen sama na kasar Sin mai suna Fujian, ya doshi yankin tekun kudancin kasar, inda ya ratsa ta zirin Taiwan, a kan hanyarsa ta gudanar da gwaje-gwaje da samar da horo.

Jami’in wanda ya bayyana hakan a Talatar nan, ya ce hakan bangare ne na ayyukan da aka saba gudanarwa lokaci-lokaci a wani bangare na kirar jirgin.

Jiang Bin, ya yi tsokacin ne yayin da yake amsa wata tambaya mai nasaba da hakan da aka yi masa, yana mai cewa, bulaguron jirgin ya dace da dokokin kasa da kasa da ayyuka masu nasaba, kuma ba shi da wata nasaba da tunkarar wani sashe. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja