Shugabannin APC sun gana gabanin babban taron jam’iyyar na ƙasa
Published: 26th, February 2025 GMT
Shugabannin Jam’iyyar APC, ciki har da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, gwamnoni, da sauran manyan jagorori, sun gana a daren Talata a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.
An gudanar da taron ne domin shirye-shiryen babban taron jam’iyyar na ƙasa da za a yi a yau a hedikwatar APC.
Kamfanin Saudiyya ya haɗa kai da gwamnatin Jigawa kan noman dabino Sanata Natasha na neman diyyar N100bn wurin AkpabioWannan shi ne taron farko da za a yi taron tun bayan hawan Shugaba Tinubu kan mulki a ranar 29 ga watan Mayu, 2023.
A bara, an tsara shirya waɗannan taruka ne a watan Satumba, amma aka ɗage su ba tare da saka sabuwar rana ba.
A baya-bayan nan, tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya soki shugabannin jam’iyyar da rashin shirya taruka, inda ya ce APC ta fara rabuwa da aƙidun da aka gina ta a kai.
An fara taron ne da misalin ƙarfe 7:30 na dare, bayan isowar Shugaba Tinubu.
Batutuwan da aka tattauna sun haɗa da shirin gudanar da babban taron jam’iyyar, matsalolin shari’a da ke shafar jam’iyyar, cibiyar nazari da tsara manufofin APC da sauransu.
Waɗanda suka halarci taron sun haɗa da Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, Shugaban Majalisar Dattawa Godswill Akpabio, Kakakin Majalisar Wakilai Tajudeen Abbas, Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje.
Sauran sun haɗa da wasu gwamnoni kamar Hope Uzodinma (Imo), Babajide Sanwo-Olu (Legas), Dapo Abiodun (Ogun), da Babagana Umar Zulum (Borno).
Haka kuma, mambobin kwamitin jam’iyyar da tsohon shugaban APC na ƙasa, Cif Bisi Akande, sun halarci taron.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
Ba wannan ne karo na farko da shugaba Trump ya nuna girman kai da rashin sani game da Afirka ba. A watan da ya gabata, lokacin da yake bayani game da dalilin da ya sa gwamnatinsa ke rage gudummawar jin kai da take bayarwa a duniya, ya ce a baya, Amurka ta samar wa kasar Lesotho gudummawar dala miliyan 8, amma “ba wanda ya taba jin sunan wannan kasa”. Amma ita wannan kasar da ko sunanta shugaba Trump bai taba ji ba, ya sanya ta cikin jerin kasashen da ya sanar da zai kakaba musu haraji, har ma ya sanya mata haraji na kaso 50%. Idan ba mu manta ba kuma, a wa’adin shugabancinsa na farko, shugaba Trump ya taba bayyana kasashen Afirka a matsayin “shithole” a lokacin da ya tabo maganar bakin haure.
Sai dai ban da girman kai da rashin sani, kalaman shugaba Trump ya kuma bayyana matsayin da gwamnatin kasar Amurka ta dade tana dauka a game da kasashen Afirka, wato a maimakon abokan hadin gwiwa na zaman daidaito da martaba juna, tana kallonsu a matsayin abin da take iya amfani da su wajen takara da sauran manyan kasashe, kuma muna iya ganin haka ne daga manufofin da mahukuntan kasar suka dauka cikin ‘yan shekarun baya.
A shekarar 2014, gwamnatin Barack Obama ta shirya taron kolin Amurka da kasashen Afirka karo na farko, inda ta dauki alkawura a gaban kasashen Afirka. Sai dai bayan taron, a maimakon ta kara samar da gudummawa, sai ta rage, har da kudaden da take samarwa a fannin yaki da cutar kanjamau a Afirka. A gun taron, Amurka ta kuma yi alkawarin zurfafa huldarta da kasashen Afirka da ma gudanar da taron a kai a kai, amma ba a sake yin taron ba har sai bayan tsawon shekaru 8. A karshen shekarar 2022, Amurka ta gudanar da taron karo na biyu, inda tsohon shugaban kasar Joe Biden ya yi alkawarin samar da iya abin da kasarsa take iya bayarwa don tabbatar da kyautata makomar Afirka, kuma a cewarsa zai kai ziyara Afirka a shekarar 2023, amma bai cika wannan alkawari ba sai zuwa karshen bara, lokacin da ya kusan sauka daga kujerar shugabanci, kuma ba mu san yaushe za a cika sauran alkawuran da ya dauka ba.
Bayan da gwamnati mai ci ta fara aiki, jerin matakan da ta dauka sun haifar da munanan illoli ga kasashen Afirka. In mun dauki misali da harajin kwastam na ramuwar gayya da ta dauka a baya bayan nan, inda ta sanya haraji mai yawa kan kasashen Afirka 51, ciki har da 50% a kan Lesotho da 47% a kan Madagascar da 40% a kan Mauritius, matakin da ya kasance tamkar yi wa kasashen fashi. Abin lura kuma shi ne, harajin ya dakatar da dokar samar da ci gaba da damammaki a Afirka da aka san ta da AGOA, tun kafin wa’adinta ya cika, lamarin da ya jefa kasashen Afirka da dama cikin mawuyacin hali wajen yin ciniki da Amurka.
Har kullum kasar Sin na ganin cewa, Afirka dandali ne na hadin gwiwar kasa da kasa, a maimakon wajen yin takara tsakanin manyan kasashe. Rashin girmamawa ne ga kasashen Afirka da al’ummarsu yadda Amurka take da rashin sanin nahiyar, kuma rashin sahihancin da take wa hadin gwiwarta da kasashen Afirka ya shaida gazarwata ta daukar kasashen Afirka da muhimmanci. Kasashen Afirka na bukatar kawaye na gaske. Idan gwamnatin Trump tana son samun karbuwa daga kasashen Afirka, dole ne ta gyara matsayinta, kuma ya kamata ta fara da fahimtar kowace kasa da ke nahiyar. (Mai Zane: Mustapha Bulama)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp