Aminiya:
2025-06-15@16:16:04 GMT

40% na matan Kano sun fuskaci cin zarafi a gida —Shugaban Majalisa

Published: 25th, February 2025 GMT

Shugaban Majalisar Wakilai, Tajuddeen Abbas, ya bayyana cewa mutum hudu a cikin kowane mata 10 a Jihar Kano sun fuskanci cin zarafi a gidajensu. 

Tajuddeen Abbas ya bayyana cewa akalla kashi 35 na matan Najeriya sun fuskanci cin zarafi, lamarin da ya ce ya fi muni a yankin Arewa maso Yamma.

Ya bayyana wa taron wayar da kai game da illar ta’ammali da miyagun kwayoyi da kuma cin zarafi a cikin gidaje cewa, “abin ya fi muni a yankin Arewa maso Yamma, inda a Jihar Kano matan da ake cin zarafinsu a cikin gidajensu sun kai kashi 40 cikin 100.

Game da yawa masu ta’mmali da miyagun kwayoyi kuwa, Shugaban Majalisar Wakilan, wanda dan yankin ne, ya bayyana cewa an samu karuwar kashi 25 cikin 100 na masu ta’ammali da miyagun kwayoyi a cikin shekaru uku da suka gabata.

Dan kwallon Najeriya ya mutu bayan fadowa daga bene a Uganda Luwadi: Magijanci ya lalata dan shekara 5 a Zariya Ya daɓa wa yayansa wuƙa saboda Naira 700

Tajudden mai wakiltar Zariya da Sabon Gari daga Jihar Kaduna, ya bayyana cewa an samu karuwar miyagun kwayoyi da jami’an tsaro suka kwace da kashi 28 cikin 100 a shekarar 2023.

Don haka ya yi kira da a dauki kwararan matakan gaggawa da kuma dabaru na musamman domin magance matsalolin cin zarafi a gidajen aure da kuma ta’ammali da miyagun kwayoyi a yankin na Arewa maso Yammak.

Ya jaddada muhimmancin hadin kan hukumomin gwamnati da da shugabannin al’umma da kungiyoyi masu zaman kansu wajen yi wa tufkar hanci.

A nasa bangaren, Shugaban Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA), Birgediya-Janar Mohamed Buba Marwa (murabsu), ya bayyan cewa a halin yanzu, daya a cikin kowane mutum hudu masu ta’ammali da miyagun kwayoyi na Najeriya, mace ce.

Buba Marwa ya c,e “mutum miliyan uku ne miyagun kwayoyi suka yi wa illa a yankin Arewa maso Yamma, daga cikin mutum miliyan 14.3 ’yan shekaru 15 zuwa 64 da ke ta’ammali da miyagun kwayoyi a Najierya.”

Amma ya ce hukumar tana kara matsa kaimi wajen yakar matsalar, inda a shekara hudu da suka gabata ta kama mutum 57,792 tare da kwale kilogram milyan 9.9 na miyagun kwayoyi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: cin zarafi Miyagun Kwayoyi ta ammali da miyagun kwayoyi ya bayyana cewa cin zarafi a

এছাড়াও পড়ুন:

Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa

Yayin da damina ke ƙara ƙaratowa, Gwamnatin Jihar Kano, ta fara wani aikin tsaftace manyan magudanan ruwa domin daƙile aukuwar ambaliyar ruwa.

An fara aikin ne a yankin shataletalen Baban Gwari, ɗaya daga cikin wuraren da ambaliya ke yawan aukuwa a Birnin Kano.

Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya

Ma’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi ce ke jagorantar aikin tsaftace magudanan ruwan.

Wannan mataki na daga cikin shirin gwamnatin jihar na kare rayuka, dukiyoyi, da kuma inganta ababen more rayuwa.

A lokacin ƙaddamar da aikin, Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi, Hashim Muhammad Dahiru, ya bayyana cewa an zaɓi Baban Gwari saboda muhimmancinsa da kuma yadda wajen yake a lokacin damina.

Ya ce wajen ya daɗe da zama wajen zubar da shara barkatai da kuma toshe hanyoyin ruwa.

Ya ƙara da cewa wannan wajen ba wai kawai muhimmiyar mahaɗa ba ce, amma kuma yana ɗaya daga cikin manyan hanyoyin ruwa da ke da alaƙa da ruwan Jakara da Kwarin Gogau.

Kwamishinan ya bayyana cewa mazauna yankin da masu wucewa sun sha fuskantar ambaliya da ta shafi rayuwarsu, lafiyarsu da kuma zirga-zirgarsu.

Ya ce wannan aikin ba na al’ada ba ce, illa alama ce da ke nuna cewa gwamnatin jihar ta ɗauki matakin kare muhalli da kuma samar da birni mai jure sauyin yanayi da ambaliya.

Ya yaba wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa jagoranci da goyon bayan da ya bai wa ma’aikatar wajen aiwatar da wannan aiki.

Ya ce gwamnatin ta amince da sanya tsaftace magudanan ruwa a matsayin aikin da za a riƙa gudanarwa a kowace shekara domin tabbatar da tsaftar hanyoyin ruwa a faɗin jihar.

Haka kuma, gwamnatin ta bayar da kwangilar gyaran shataletalen Baban Gwari domin inganta zirga-zirga da rage yawan ambaliya, ta hanyar gina sabbin hanyoyin ruwa.

Kwamishinan ya bayyana cewa waɗannan matakai suna nuna irin hangen nesa da damuwar gwamnan jihar kan lafiyar jama’a da kuma kare su daga illolin da ke zuwa da ambaliya da sauyin yanayi.

Ya buƙaci jama’a da su daina zubar da shara barkatai, musamman a cikin magudanan ruwa, ya kuma buƙaci su riƙa ɗaukar nauyin tsaftace muhallinsu.

Ya ce gwamnatin za ta yi nata aikin, amma ana buƙatar haɗin gwiwar kowa da kowa domin a cimma nasara.

Ya kuma buƙaci ma’aikata da abokan aikin muhalli da su gudanar da aikinsu da kulawa da gaskiya, yana mai cewa aikin ba wai tsaftace magudanan ruwa ba ne kawai, amma aikin ne na kare rayuka, daƙile haɗura da kuma gina sabuwar Kano mai tsafta da lafiya.

A ’yan shekarun nan, yankin Baban Gwari ya yi ƙaurin suna wajen yawan aukuwar ambaliya, har ma da rasa rayuka da dukiyoyi.

Wannan ya sa gwamnatin jihar ta ɗauki matakin gaggawa domin magance matsalar kafin saukar daminar bana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna