40% na matan Kano sun fuskaci cin zarafi a gida —Shugaban Majalisa
Published: 25th, February 2025 GMT
Shugaban Majalisar Wakilai, Tajuddeen Abbas, ya bayyana cewa mutum hudu a cikin kowane mata 10 a Jihar Kano sun fuskanci cin zarafi a gidajensu.
Tajuddeen Abbas ya bayyana cewa akalla kashi 35 na matan Najeriya sun fuskanci cin zarafi, lamarin da ya ce ya fi muni a yankin Arewa maso Yamma.
Ya bayyana wa taron wayar da kai game da illar ta’ammali da miyagun kwayoyi da kuma cin zarafi a cikin gidaje cewa, “abin ya fi muni a yankin Arewa maso Yamma, inda a Jihar Kano matan da ake cin zarafinsu a cikin gidajensu sun kai kashi 40 cikin 100.
Game da yawa masu ta’mmali da miyagun kwayoyi kuwa, Shugaban Majalisar Wakilan, wanda dan yankin ne, ya bayyana cewa an samu karuwar kashi 25 cikin 100 na masu ta’ammali da miyagun kwayoyi a cikin shekaru uku da suka gabata.
Dan kwallon Najeriya ya mutu bayan fadowa daga bene a Uganda Luwadi: Magijanci ya lalata dan shekara 5 a Zariya Ya daɓa wa yayansa wuƙa saboda Naira 700Tajudden mai wakiltar Zariya da Sabon Gari daga Jihar Kaduna, ya bayyana cewa an samu karuwar miyagun kwayoyi da jami’an tsaro suka kwace da kashi 28 cikin 100 a shekarar 2023.
Don haka ya yi kira da a dauki kwararan matakan gaggawa da kuma dabaru na musamman domin magance matsalolin cin zarafi a gidajen aure da kuma ta’ammali da miyagun kwayoyi a yankin na Arewa maso Yammak.
Ya jaddada muhimmancin hadin kan hukumomin gwamnati da da shugabannin al’umma da kungiyoyi masu zaman kansu wajen yi wa tufkar hanci.
A nasa bangaren, Shugaban Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA), Birgediya-Janar Mohamed Buba Marwa (murabsu), ya bayyan cewa a halin yanzu, daya a cikin kowane mutum hudu masu ta’ammali da miyagun kwayoyi na Najeriya, mace ce.
Buba Marwa ya c,e “mutum miliyan uku ne miyagun kwayoyi suka yi wa illa a yankin Arewa maso Yamma, daga cikin mutum miliyan 14.3 ’yan shekaru 15 zuwa 64 da ke ta’ammali da miyagun kwayoyi a Najierya.”
Amma ya ce hukumar tana kara matsa kaimi wajen yakar matsalar, inda a shekara hudu da suka gabata ta kama mutum 57,792 tare da kwale kilogram milyan 9.9 na miyagun kwayoyi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: cin zarafi Miyagun Kwayoyi ta ammali da miyagun kwayoyi ya bayyana cewa cin zarafi a
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe mafarauta 10 a Adamawa
Aƙalla wasu mutum 10 mafarauta sun rasa rayukansu yayin aikin ceto a ƙauyen Kopire da ke Ƙaramar Hukumar Hong ta Jihar Adamawa.
Shugaban ƙungiyar mafarautan Nijeriya reshen Arewa maso Gabas, Shawulu Yohanna ne ya tabbatar wa Aminiya hakan a ranar Talata.
Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno An dawo da wutar lantarki a Sifaniya da PortugalA cewarsa, ajali ya katse hanzarin mafarautan ne yayin wani arbatu da mayaƙan Boko Haram da suka yi musu kwanton ɓauna a jeji.
Ya bayyana cewa, mafarautan sun tunkari maharan ne bayan samun bayanan sirri da ke nuna cewa suna shirin kai hari.
“Abin takaicin shi yadda ake yi wa Gwamnan Borno ƙafar ungulu a ƙoƙarin da yake yi na ganin an kawo ƙarshen wannan hare-hare a yankin,” in ji shi.
Yohanna ya bayyana damuwa kan yadda mayaƙan Boko Haram ke ci gaba da ƙara ƙarfi a bayan nan da ke zama abin fargaba ga mazauna yankunan da abin ya shafa.
“Mun samu labarin cewa wani jirgi mai saukar ungulu ne yake jigilar mayaƙan daga sansaninsu zuwa wuraren da suke sheƙe ayarsu ba tare fuskantar wata tirjiya ba.
“Amma ina mai tabbatar da cewa muddin Gwamnatin Tarayya ta ɗauki mataki ta hanyar tanadar makamai na zamani, za a kawo ƙarshen waɗannan maƙiya cikin lokacin ƙanƙani.”
Ya roƙi Gwamnatin Tarayya da ta tanadar wa mafarauta da ’yan sa-kai manyan makamai na zamani domin kawo ƙarshen mayaƙan Boko Haram a yankin.
Wannan harin dai na zuwa ne ƙasa da sa’o’i 12 da wasu ’yan ta’adda suka kashe fiye da mutum 30 ciki har da mata da ƙananan yara a ƙananan hukumomin Kala Balge da Gambarou Ngala da ke jihar.