Aminiya:
2025-07-31@17:30:52 GMT

40% na matan Kano sun fuskaci cin zarafi a gida —Shugaban Majalisa

Published: 25th, February 2025 GMT

Shugaban Majalisar Wakilai, Tajuddeen Abbas, ya bayyana cewa mutum hudu a cikin kowane mata 10 a Jihar Kano sun fuskanci cin zarafi a gidajensu. 

Tajuddeen Abbas ya bayyana cewa akalla kashi 35 na matan Najeriya sun fuskanci cin zarafi, lamarin da ya ce ya fi muni a yankin Arewa maso Yamma.

Ya bayyana wa taron wayar da kai game da illar ta’ammali da miyagun kwayoyi da kuma cin zarafi a cikin gidaje cewa, “abin ya fi muni a yankin Arewa maso Yamma, inda a Jihar Kano matan da ake cin zarafinsu a cikin gidajensu sun kai kashi 40 cikin 100.

Game da yawa masu ta’mmali da miyagun kwayoyi kuwa, Shugaban Majalisar Wakilan, wanda dan yankin ne, ya bayyana cewa an samu karuwar kashi 25 cikin 100 na masu ta’ammali da miyagun kwayoyi a cikin shekaru uku da suka gabata.

Dan kwallon Najeriya ya mutu bayan fadowa daga bene a Uganda Luwadi: Magijanci ya lalata dan shekara 5 a Zariya Ya daɓa wa yayansa wuƙa saboda Naira 700

Tajudden mai wakiltar Zariya da Sabon Gari daga Jihar Kaduna, ya bayyana cewa an samu karuwar miyagun kwayoyi da jami’an tsaro suka kwace da kashi 28 cikin 100 a shekarar 2023.

Don haka ya yi kira da a dauki kwararan matakan gaggawa da kuma dabaru na musamman domin magance matsalolin cin zarafi a gidajen aure da kuma ta’ammali da miyagun kwayoyi a yankin na Arewa maso Yammak.

Ya jaddada muhimmancin hadin kan hukumomin gwamnati da da shugabannin al’umma da kungiyoyi masu zaman kansu wajen yi wa tufkar hanci.

A nasa bangaren, Shugaban Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA), Birgediya-Janar Mohamed Buba Marwa (murabsu), ya bayyan cewa a halin yanzu, daya a cikin kowane mutum hudu masu ta’ammali da miyagun kwayoyi na Najeriya, mace ce.

Buba Marwa ya c,e “mutum miliyan uku ne miyagun kwayoyi suka yi wa illa a yankin Arewa maso Yamma, daga cikin mutum miliyan 14.3 ’yan shekaru 15 zuwa 64 da ke ta’ammali da miyagun kwayoyi a Najierya.”

Amma ya ce hukumar tana kara matsa kaimi wajen yakar matsalar, inda a shekara hudu da suka gabata ta kama mutum 57,792 tare da kwale kilogram milyan 9.9 na miyagun kwayoyi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: cin zarafi Miyagun Kwayoyi ta ammali da miyagun kwayoyi ya bayyana cewa cin zarafi a

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Mata a Arewacin Najeriya na fuskantar kalubale da dama a fannin karantar kimiyya.

Akwai darussan da a mafi yawan lokuta ba mata kadai ba, har da mazan na kaurace musu.

NAJERIYA A YAU: Matakan Da Muke Dauka Don Karfafawa ’Yan Najeriya Kwarin Gwiwar Kada Kuri’a —INEC DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta

Shirin Najeriya a Yau ya yi nazari  ne kan dalilan da suka sa matan Arewacin Najeriya ke tsoron karantar ilimin kimiyya.

Domin sauke cikakken shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Kula da Da’ar Ma’aikata Za Ta Fara Daukar Bayanai Ta Yanar Gizo
  • Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Majalisa ta ba NNPCL mako uku ya yi mata bayanin inda tirilyan 210 ta shiga
  • Kwamitin Aikin Hajjin 2025 Na Jihar Kano Ya Kammala Rahoton Aikinsa Na Wucin Gadi
  • Kwale-kwale Ya Kife Da Fasinjoji 16 A Karamar Hukumar Taura
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya
  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa