Babu hannun Naira Marley a mutuwar Mohbad — Kotu
Published: 25th, February 2025 GMT
Kotun Majistire da ke zama a Sabo a unguwar Yaba ta Jihar Legas ta wanke mawaƙi Abdulazeez Fashola, wanda aka fi sani da Naira Marley da abokin aikinsa Samson Balogun Eletu, wato Sam Larry daga zargin hannu a mutuwar mawaƙi Aloba Oladimeji IleriOluwa, wanda aka fi sani da Mohbad.
Mai Shari’a Ejiro Kubenje, wanda ya karanta hukuncin ya ce babu wata ayar tambaya kan mutanen biyu game da rasuwar Mohbad.
Haka nan ma kotun ta sallami Oodunni Ibrahim, wanda ake kira Primeboy da tsohon manajan Mohbad, Opere Babatunde.
Sai dai hukuncin ya ce za a gurfanar da ma’aikaciyar jinyar da ta kula da Mohbad gabanin mutuwarsa, wato Feyisayo Ogedengbe, da ɗaya daga cikin abokan marigayin, Ayobami Sadiq bisa tuhumar su da sakaci, wanda ya kai ga mutuwar matashin mawaƙin.
Ana iya tuna cewa, mutuwar Mohbad a shekarar 2023 dai ta janyo ce-ce-ku-ce matuƙa musamman a kafafen sada zumunta na zamani a ciki da wajen Nijeriya.
Kazalika, a wancan lokacin an gudanar da zanga-zanga a jihohin Legas da Oyo da Delta, don neman a binciki musabbabin mutuwar ta shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Naira Marley
এছাড়াও পড়ুন:
Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya bayyana a yau Litinin cewa, babu wata tattaunawa da aka yi ta wayar tarho tsakanin shugabannin kasashen Sin da Amurka a baya-baya nan, haka kuma bangarorin biyu ba su cimma wata yarjejeniya ko su tuntubi juna game da batun haraji ba. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp