HausaTv:
2025-06-15@23:32:08 GMT

Iran : Makaman Kare Dangi Na Israila Barazana Ne Ga Zaman Lafiya Da Tsaro

Published: 25th, February 2025 GMT

Iran ta bakin Ministan harkokin wajen kasar Abbas Araghchi ta shaidawa taron kwance damarar makamai na Majalisar Dinkin Duniya a Geneva cewa, makaman kare dangi na gwamnatin Isra’ila da suka hada da makaman nukiliya na ci gaba da yin barazana ga zaman lafiya da tsaro a yankin da ma duniya baki daya.

A yayin jawabin da ya yi a ranar Litinin, a babban taro na 2025 kan kwance damara, a hedkwatar MDD dake Geneva, Mr.

Araghchi ya yi kira ga kasashen duniya da MDD da su ba da fifiko kan batun kawar da makaman nukiliya.

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa “dole ne kasashen duniya su tilastawa Isra’ila bin yarjejeniyar hana yaduwar makaman kare dangi (NPT) don kawar da dukkanin ayyukanta na nukiliya na kasa da kasa.

A yayin da yake bayyana damuwarsa kan barazanar makaman nukiliya da kuma mummunar illar da suke yi ga bil’adama da muhalli, Mr. Araghchi ya yi kira da a sanya makaman nukiliya a kan gaba wajen damuwar kasashen duniya da MDD.

Araghchi ya bayyana irin ayyukan da ba a taba ganin irinsa ba, da suka hada da kisan kare dangi, laifuffukan yaki da laifukan cin zarafin bil Adama da gwamnatin Isra’ila ta aikata a zirin Gaza, wanda ya yi sanadin lalata yankunan da aka yi wa kawanya tare da mutuwar dubban mutane, musamman mata, yara da kuma tsofaffi.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: makaman nukiliya

এছাড়াও পড়ুন:

Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada

A sandiyyar harin da ‘yan sahayoniya su ka kawo wa Iran da asubahin yau, masana fasaahr Nukiliya da dama sun yi shahada.

Kamfanin dillancin labarun “Mehr” na Iran ya ambaci cewa: Daga cikin wadanda su ka yi shahadar da akwai tsohon shugaban hukumar makamashin Nukiliya ta Iran; Faridun Abbasi. Shugaban jami’ar Azad, Muhammad Mahdi Dahranji. Shugaban Kwalejin fasahar Nukiliya, Abdulhamid Minochehri. Hakan nan kuma Malamin fasahar Nukiliya Ahmda Riza Zulfiqar, sai mataimakin shugaban hukumar  makamashin Nukiliya Amir Husain Fiqhi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Birgediya Pakphur: Nan Gaba Kadan Za A Budewa “Isra’ila” Kofofin Jahannama
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje