Aminiya:
2025-09-18@08:25:41 GMT

An yi zanga-zangar kisan ɗalibi a Jami’ar FUDMA da ke Katsina

Published: 24th, February 2025 GMT

A wannan Litinin ɗin ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Dutsinma FUDMA suka shiga rana ta biyu ta zanga-zangar kisan wani ɗalibi da ake zargin jami’an bijilanti na JTF sun yi a ranar Lahadi.

Aminiya ta samu rahoton cewa ’yan bijilantin sun buɗe wa wasu ɗalibai da ke tafe kan babur wuta ba tare da sun tsayar da su domin tuhuma bisa zargin cewa masu yi wa ’yan bindigar daji leƙen asiri ne.

NNPP ta dakatar da Kawu Sumaila da Ali Madakin Gini Mun gano inda Bello Turji ya ɓoye —Sojoji

Wannan harbin da suka yi ya yi sanadiyar mutuwar wannan ɗalibi mai suna Saidu Abdulkadir.

Ana iya tuna cewa, a kwanakin baya an kama wani ɗalibin jami’ar yana safarar makamai.

Bayanai sun ce hakan ne ya sanya wasu ke tunanin ’yan bijilantin sun yi amfani da wancan lamari da ya faru har suka aikata abin da ya yi sanadiyar mutuwar wannan ɗalibi a yanzu.

Dangane da hakan ne ɗaliban ke zanga-zangar neman a gudanar da bincike tare gurfanar da waɗanda suka yi wannan kisa hukuncin da ya dace don tabbatar da adalci.

Kakakin rundunar ’yan sandan Katsina, DSP Abubakar Sadiq Aliyu ya tabbatar da faruwar hakan kuma ya ce suna kan binciken lamarin.

Ɗalibai suna zanga-zangar kisan ɗalibi a FUDMA.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗalibi Jami ar FUDMA Jihar Katsina zanga zangar

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin Jiang Bin, ya ce a baya bayan nan babban jirgin ruwan dakon jiragen sama na kasar Sin mai suna Fujian, ya doshi yankin tekun kudancin kasar, inda ya ratsa ta zirin Taiwan, a kan hanyarsa ta gudanar da gwaje-gwaje da samar da horo.

Jami’in wanda ya bayyana hakan a Talatar nan, ya ce hakan bangare ne na ayyukan da aka saba gudanarwa lokaci-lokaci a wani bangare na kirar jirgin.

Jiang Bin, ya yi tsokacin ne yayin da yake amsa wata tambaya mai nasaba da hakan da aka yi masa, yana mai cewa, bulaguron jirgin ya dace da dokokin kasa da kasa da ayyuka masu nasaba, kuma ba shi da wata nasaba da tunkarar wani sashe. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Pezeshkian: Iran da Masar suna da tsohon tarihi a duniya
  • ’Yan bindiga sun sako ma’auratan da suka sace a Katsina bayan biyan N50m
  • Gobara ta kashe manyan jami’an hukumar FIRS 4 a Legas
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000