Kar A Ji Tsoron Aikace-Aikacen Kasar Amurka
Published: 24th, February 2025 GMT
To, ma iya cewa kasar Amurka ta riga ta fusata dukkan kasashen duniya. Idan an sa wata kasar dake nahiyar Afirka fuskantar matakin da kasar Amurka ta dauka ita kadai, to, za ta ji akwai matsin lamba. Sai dai yanzu za a saki jiki, saboda ko da yake kasar Amurka ta kan ci zarafin sauran kasashe, amma ba ta da karfin cin zarafin dukkan kasashe a sa’i daya.
Ban da halartar taron tsaro a Munich a wannan karo, Wang Yi ya kuma shugabanci taron kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya, da halartar taron ministocin waje na rukunin kasashe 20 (G20), duk a kwanakin baya. Inda ya jaddada manufofin Sin na aiwatar da ra’ayin kasancewar bangarori masu fada-a-ji da yawa a duniya, da tsayawa kan daidaituwa, da adalci, da hadin kai, gami da neman zaman lafiya da ci gaban tattalin arziki, da hadin gwiwa don tabbatar da moriyar juna, da dai sauransu. Mahalarta tarukan sun nuna yabo kan jawaban ministan na kasar Sin, ganin yadda maganarsa ta kwantar da hankalinsu. Saboda ta nuna cewa, kasar Sin har kullum tana samar da tabbaci ga tsare-tsaren duniya, da ba da gudunmowa a kokarin tabbatar da ci gaban harkokin duniya.
Ban da haka, Wang Yi ya gana da takwaransa na kasar Angola, dake shugabantar kungiyar kasashen Afirka ta AU a karba-karba, Tete Antonio. Inda Wang ya ce, “‘Yan uwa Sinawa dake nahiyar Afirka sun san wace ce kawa ta gaske ta Afirka. “Wannan wata tsohuwar magana ce, amma yanzu ta nuna ma’ana mai zurfi.
Haka zalika, Wang ya ce, “A yunkurin kasashen Afirka na raya kai a nan gaba, kasar Sin za ta ci gaba da kokarin ba da taimako a matsayin wata sahihiyar abokiya.” Tabbas, za a iya tabbatar da makomar Afirka mai haske, bisa hadin kanta da kasar Sin, da huldar cude-ni-in-cude-ka dake tsakanin daukacin kasashe masu tasowa. (Bello Wang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: kasar Amurka
এছাড়াও পড়ুন:
Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce za a yi taro karo na hudu na shawarwari tsakanin Tehran da Washington kan shirin nukiliyar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a birnin Rome na kasar Italiya a ranar Asabar mai zuwa.
M. Araghchi ya fadawa manema labarai a gefen taron majalisar ministocin gwamnatin kasar na mako-mako yau Laraba cewa, inda ya ce taron na Rome zai kasance gabanin wani taro a ranar Juma’a na tsakanin Tehran da kasashen Turan nan uku da ake wa lakabi da E3 wato – Ingila, Faransa da kuma Jamus wadanda suka sanya hannu kan yarjejeniyar nukiliyar Iran ta 2015.
Ya ce rawar da kasashen Turai uku ke takawa ta ragu sakamakon manufofinsu a tattaunawar da aka dade ana yi, don haka a shirye muke mu gudanar da zagaye na gaba na shawarwari da su a birnin Rome.
Babban jami’in diflomasiyyar ya kara da cewa, Tehran na da burin warware batun nukiliyarta cikin lumana.”
Da aka tambaye shi game da halin da ake ciki na baya-bayan nan na kudaden da Iran ta toshe saboda takunkumin da kasashen yamma suka kakaba mata, Araghchi ya ce daskararrun kudaden na daga cikin takunkumin da ya zama dole a dagewa iran.
Kawo yanzu Iran da Amurka sun yi tattaunawa har uku ta farko a Oman, ta biyu a Italiya sai kuma wace aka gudanar a ranar Asabar data gabata a Oman.
Dukkanin bangarorin na cewa akwai fata mai kyau a jerin tattaunawar da suka gabata.