Aminiya:
2025-06-15@18:01:56 GMT

An kama mutum biyu kan kisan wata mata saboda maita

Published: 23rd, February 2025 GMT

Rundunar ‘yan sandan yankin Biu ta tsare wasu mutane biyu da ake zargi da kashe wata mata ‘yar shekara 50 da ake zargi da bokanci da maita.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Borno, Yusuf Lawan ya tabbatar da hakan ga manema labarai a Maiduguri.

Ɗan shekara 43 ya auri mai shekara 88 Yadda ƙananan yara ke zaman kurkuku ba tare an da kai su kotu ba

Kwamishinan ya ce an kashe matar mai suna Hajara Saleh ne a ranar 21 ga watan Fabrairu a unguwar Bantine da ke Ƙaramar Hukumar Biu ta Jihar Borno.

Kwamishinan ya bayyana cewar, waɗanda ake zargin — Ja’o Muhammad da Idris Muhammad — sun yi tarayya wajen kashe matar a dalilin zargin maita da suke mata.

Lawan ya ce matar ta samu raunuka a wuyanta, kafafu, da hannayenta, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwarta.

Ya ce wani mazaunin unguwar Dadinkowa Gunda ne ya kai wa ’yan sanda rahoton faruwar lamarin da misalin karfe 11:00 na safiyar ranar.

“Da isa wurin da lamarin ya faru, jami’anmu sun gano cewa mijin nata Saleh Bole da sauran ‘yan uwa sun rigaya sun binne ta kamar yadda addinin musulunci ya tanada,” in ji kwamishinan.

Ya ƙara bayyana cewa, duk da jana’izar da aka yi wa matar amma jami’an ‘yan sanda sun yi nasarar ɗaukar hoton gawar marigayiyar tare da tattara muhimman shaidu.

Kwamishinan ya bayyana abin da ya faru a matsayin dabbanci da rashin gaskiya, yana mai gargaɗin cewa bai kamata a yi amfani da zargin maita a matsayin hujjar tashin hankali ko kisan gilla ba.

“Rundunar ‘yan sanda ta jajirce wajen gurfanar da duk wadanda suka aikata wannan danyen aiki a gaban kuliya.

“Don haka ya kamata jama’a su fahimci cewa doka ba ta ba mutane damar ɗaukar al’amura a hannunsu ba,” inji shi

A cewarsa, waɗanda ake zargin suna fuskantar tuhuma da suka haɗa baki, kisan kai, da sauran laifuka masu alaƙa da su, inda ya ce za a gurfanar da su gaban kuliya da zarar an kammala bincike.

Lawan ya buƙaci al’umma da su kai rahoton zargin bokanci ko duk wasu korafe-korafe ga ‘yan sanda maimakon ɗaukar doka a hannu.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda jihar Borno

এছাড়াও পড়ুন:

Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8

Kwanaki takwas bayan wata mummunar ambaliyar ruwa da ta mamaye garin Mokwa, hedikwatar Ƙaramar hukumar Mokwa a Jihar Neja, an gano gawar mutum ɗaya daga cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su.

Mazauna garin sun shaida wa Daily Trust cewa, an tsinci gawar ne a ranar Alhamis a wata gona da ke kan hanyar wucewa kusa da wani wuri da aka fi sani da ‘dam’.

Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi

A cewar shaidun gani da ido, an kasa tantance wanda abin ya shafa saboda gawar ta lalace. An binne shi ne a inda aka gano gawarsa.

Wata mazauniyar yankin mai suna Tswata Mai Rubutu da ta zanta da Aminiya ta wayar tarho, ta ce an tsinci gawar a kan hanyar da ruwa ke wucewa.

“Gawar wani babban mutum ne, amma ba za mu iya gane shi ba saboda tuni ya fara lalacewa. An binne shi a wurin tun da ba a iya motsa gawar,” in ji shi.

An yi ƙoƙarin jin ta bakin Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, Abdullahi Baba Arah, domin ƙarin bayani lamarin ya ci tura.

Tun da farko hukumar ta tabbatar da mutuwar mutane 161, yayin da wasu da dama suka ɓace bayan iftila’in ambaliyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran