An kama mutum biyu kan kisan wata mata saboda maita
Published: 23rd, February 2025 GMT
Rundunar ‘yan sandan yankin Biu ta tsare wasu mutane biyu da ake zargi da kashe wata mata ‘yar shekara 50 da ake zargi da bokanci da maita.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Borno, Yusuf Lawan ya tabbatar da hakan ga manema labarai a Maiduguri.
Ɗan shekara 43 ya auri mai shekara 88 Yadda ƙananan yara ke zaman kurkuku ba tare an da kai su kotu baKwamishinan ya ce an kashe matar mai suna Hajara Saleh ne a ranar 21 ga watan Fabrairu a unguwar Bantine da ke Ƙaramar Hukumar Biu ta Jihar Borno.
Kwamishinan ya bayyana cewar, waɗanda ake zargin — Ja’o Muhammad da Idris Muhammad — sun yi tarayya wajen kashe matar a dalilin zargin maita da suke mata.
Lawan ya ce matar ta samu raunuka a wuyanta, kafafu, da hannayenta, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwarta.
Ya ce wani mazaunin unguwar Dadinkowa Gunda ne ya kai wa ’yan sanda rahoton faruwar lamarin da misalin karfe 11:00 na safiyar ranar.
“Da isa wurin da lamarin ya faru, jami’anmu sun gano cewa mijin nata Saleh Bole da sauran ‘yan uwa sun rigaya sun binne ta kamar yadda addinin musulunci ya tanada,” in ji kwamishinan.
Ya ƙara bayyana cewa, duk da jana’izar da aka yi wa matar amma jami’an ‘yan sanda sun yi nasarar ɗaukar hoton gawar marigayiyar tare da tattara muhimman shaidu.
Kwamishinan ya bayyana abin da ya faru a matsayin dabbanci da rashin gaskiya, yana mai gargaɗin cewa bai kamata a yi amfani da zargin maita a matsayin hujjar tashin hankali ko kisan gilla ba.
“Rundunar ‘yan sanda ta jajirce wajen gurfanar da duk wadanda suka aikata wannan danyen aiki a gaban kuliya.
“Don haka ya kamata jama’a su fahimci cewa doka ba ta ba mutane damar ɗaukar al’amura a hannunsu ba,” inji shi
A cewarsa, waɗanda ake zargin suna fuskantar tuhuma da suka haɗa baki, kisan kai, da sauran laifuka masu alaƙa da su, inda ya ce za a gurfanar da su gaban kuliya da zarar an kammala bincike.
Lawan ya buƙaci al’umma da su kai rahoton zargin bokanci ko duk wasu korafe-korafe ga ‘yan sanda maimakon ɗaukar doka a hannu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda jihar Borno
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
Daga Usman Muhammad Zaria
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.
Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.
Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen tsaro.
CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.