HausaTv:
2025-07-31@16:16:41 GMT

Jami’an Diblomasiyya Daga Kungiyar G20 Da Dama Sun Isa Afrika Ta Kudu

Published: 21st, February 2025 GMT

Jami’an diblomasiyya da dama daga kasashen kungiyar G20 ne suka isa birnin Johannesburg na kasar Afirka ta kudu, don halattar taro na kwanaki biyu.

Ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Lavrov ya isa birnin Johannesburg a jiya Alhamis kwanaki biyu kacal da ya gana da tokwaransa na kasar Amurka a birnin Riyad na kasar Saudiya.

Shafin yanar gizo na labarai ‘Africa News’ yace ana saran kasashen turai zasu kara jaddada goyon bayansu ga kasar Ukraine a yakin da take fafatawa da kasar Rasha. Duk tare da cewa gwamnatin kasar Amurka tana son kawo karshen yakin ba tare da su ba.

Kasashen Burtaniya , Faransa, Jamus da kuma tarayyar Turai EU gaba daya suna goyon bayan Ukraine a yakinta da Rasha.

Har’ila yau sakataren harkokin wajen Amurka Marco Rubio  bai bayyana a taron ba. Sai dai ana zaton jakadan kasar Amurka a kasar Afirka ta kudu  Dana Brown ne zata wakilci kasar a taron.

Amurka ta ki halattar taron G20 A Afrika ta Kudu ne saboda matsayinta dangane da yaki a Gaza da kuma wasu dokokin mallaka a kasarsa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyar Mutuwar Mutane Da Dama A Yola

Ruwan sama mai ƙarfn gaske ya haddasa mummunar ambaliya a Yola ta Kudu, Jihar Adamawa, inda mutane da dama suka mutu, yayin da wasu da dama suka rasa matsugunnansu.

Yankunan da ambaliyar ta fi shafa sun hada da Shagari, Sabon Pegi da Anguwan Tabo.

Ayyukan ceto suna ci gaba da gudana, inda Sojoji da hukumomin agaji ke kwashe mazauna yankunan da abin ya shafa.

Hukumomi sun shawarci mazauna yankunan da ke fuskantar barazanar ambaliya da su gaggauta barin wuraren, kasancewar ana hasashen karin ruwan sama.

 

RN

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Kakabawa Jami’an Gwamnatin Falasdinawa Takunkuman Hana Shiga Amurka
  • Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine
  • Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran
  • Jami’an Tsaron Katsina Sama Da 100 Sun Rasu A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda – Gwamnati
  • Hamas: HKI Da Amurka Sun Janye Daga Tattaunawa Ne Don Sake Damarar Yaki
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan
  • Shugaban Kasar Masar Ya Roki Trump Ya Kawo Karshen Yaki A Gaza
  • Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyar Mutuwar Mutane Da Dama A Yola