Ba ni da hannu a kisan Dele Giwa — Janar Babangida
Published: 21st, February 2025 GMT
Tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida ta nesanta hannunsa da kisan gogaggen ɗan jarida kuma Babban Editan Jaridar Newawatch, Dele Giwa.
An kashe Dele Giwa wanda fitaccen mai sukar gwamnatin Babangida ne, ta hanyar wasikar bom a gidansa da ke Legas a ranar 19 ga watan Oktoban 1986.
Kwana biyu kafin kisan nasa wani babban jami’in Rundunar Leƙen Asiri ta Soji ya zargi Dele Giwa da yin fasa-kwaurin makamai da ƙasashen da nufin tayar da zaune tsaye a Najeriya
Sakamakon haka, dan jaridar ya yi hanzarin sanar da lauyansa, Gani Fawehinmi, game da halin da ake ciki.
Na yi nadamar soke zaɓen 1993 — Babangida NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ba Za Mu Sauke Farashin Burodi Ba —’Yan kasuwaAmma bayan kwanan biyu, wani babban hafsan soji, Kamar Halilu Akilu, ya kira waya ta ba Dele Giwa tabbacin cewa kuskure aka samu kuma an gano ainihin lamarin, don haka ya kwantar da hankalinsa, komai ya wuce.
Wani abokin Dele Giwa a Newawatch mai suna Ray Ekpu, ya ce bayan ’yan sa’o’i ne aka kai wani sako gwamnati gidan Dele Giwa.
Ray Ekpu ya bayyana cewa ɗan Dele Giwa mai suna Billy ne ya karbi sakon mai ɗauke da tambarin Fadar Shugaban Ƙasar ya mika wa mahaifin nasa, wanda a lokacin yake cin abinci tare da wakilin Newawatch na London, Kayode Soyinka, wand ya kawo mishi ziyara.
Wasikar mai ɗauke da tambarin Fadar Shugaban Ƙasa na kuma dauke da rubutun “wanda aka aika wa kaɗai zai buɗe.”
Amma a yanzu shekara 41 bayan kisan na Dele, Janar Babangida ya nesanta hannunsa ko masaniyar lamarin.
Babangida ya nesanta kansa da lamarin ne a littafin Tarihi da da ya ƙaddamar a ranar Alhamis a Abuja.
Babangida ya bayyana fatan cewa wata rana gaskiya ta yi halintama gano hakikanin musabbabin mutuwar Dele Giwa.
Ya bayyana takaici cewa ’yan jarida sun kawo koma baya ga binciken kisan, inda suka yi saurin yanke hukunci kafin a kammala binciken.
A cewarsa, ya yi fatan a lokacin da gwamantin farar hula ta Olusegun Obasanjo ta sake buɗe binciken kisan Dele Giwa ’yan sanda za su samo sabbin hujjoji da ke nuna abin da ya faru, amma hakan bai samu ba.উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dele Giwa kisan Dele Giwa
এছাড়াও পড়ুন:
Yarima Mai Jiran Gadon Saudiyya Ya Jaddada Goyon Bayan Kasarsa Ga Iran
Yarima mai jiran gadon Saudiyya ya tabbatarwa shugaban kasar Iran cewa: Saudiyya tana goyon bayan Iran
Yariman mai jiran gadon Saudiyya Mohammed bin Salman ya tabbatar da hakan ne a wata tattaunawa ta wayar tarho da shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian a yammacin jiya Asabar, yana mai jaddada cewa: Masarautar Saudiyya da daukacin al’ummar musulmin duniya sun hadu a kan goyon bayan Iran.
Yarima mai jiran gadon sarautar Saudiyya ya ce: Dukkanin al’ummomin kasashen musulmi a yau suna da hadin kai da jaddada goyon bayansu ga Iran, kuma yana iyaka kokarinsa a fagen diflomasiyya da matsin lamba na kasa da kasa don dakatar da wuce gona da irin da ‘yan sahayoniyya suke yi kan Iran.
Bin Salman ya yi Allah wadai da hare-haren rashin adalci da ‘yan sahayoniyya suke kaiwa Iran.
Ya kuma bayyana jimaminsa tare da jajantawa al’ummar kasar Iran dangane da wadannan hare-hare da suka rutsa da su, yana mai jaddada cewa: Saudiyya tana da tabbataccen matsayi kan tsayawa tare da ‘yar uwarta Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma duniyar musulmi a yau ta hade kan muryar daya wajen goyon bayan Iran.
Ya ci gaba da cewa: “Mun yi imanin cewa, gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila na neman ta hanyar kara kunna wutar rikici ta janyo Amurka a cikin tsakiyar rikici, amma suna da yakinin cewa martanin Iran a kan ma’aunin daidaito da matakan hankali zai dakile wannan yunƙurin makirci.”
Bin Salman ya kuma jaddada cewa: Kasarsa ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen bayar da duk wani tallafi da ya dace ga ‘yan uwanta Iran.