Aminiya:
2025-11-03@08:13:37 GMT

Ba ni da hannu a kisan Dele Giwa — Janar Babangida

Published: 21st, February 2025 GMT

Tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida ta nesanta hannunsa da kisan gogaggen ɗan jarida kuma Babban Editan Jaridar Newawatch, Dele Giwa.

An kashe Dele Giwa wanda fitaccen mai sukar gwamnatin Babangida ne, ta hanyar wasikar bom a gidansa da ke Legas a ranar 19 ga watan Oktoban 1986.

Kwana biyu kafin kisan nasa wani babban jami’in Rundunar Leƙen Asiri ta Soji ya zargi Dele Giwa da yin fasa-kwaurin makamai da ƙasashen da nufin tayar da zaune tsaye a Najeriya

Sakamakon haka, dan jaridar ya yi hanzarin sanar da lauyansa, Gani Fawehinmi, game da halin da ake ciki.

Na yi nadamar soke zaɓen 1993 — Babangida NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ba Za Mu Sauke Farashin Burodi Ba —’Yan kasuwa

Amma bayan kwanan biyu, wani babban hafsan soji, Kamar Halilu Akilu, ya kira waya ta ba Dele Giwa tabbacin cewa kuskure aka samu kuma an gano ainihin lamarin, don haka ya kwantar da hankalinsa, komai ya wuce.

Wani abokin Dele Giwa a Newawatch mai suna  Ray Ekpu, ya ce bayan ’yan sa’o’i ne aka kai wani sako gwamnati gidan Dele Giwa.

Ray Ekpu ya bayyana cewa ɗan Dele Giwa mai suna Billy ne ya karbi sakon mai ɗauke da tambarin Fadar Shugaban Ƙasar ya mika wa mahaifin nasa, wanda a lokacin yake cin abinci tare da wakilin Newawatch na London, Kayode Soyinka,  wand ya kawo mishi ziyara.

Wasikar mai ɗauke da tambarin Fadar Shugaban Ƙasa na kuma dauke da rubutun “wanda aka aika wa kaɗai zai buɗe.”

Amma a yanzu shekara 41 bayan kisan na Dele, Janar Babangida ya nesanta hannunsa ko masaniyar lamarin.

Babangida ya nesanta kansa da lamarin ne a littafin Tarihi da da ya ƙaddamar a ranar Alhamis a Abuja.

Babangida ya bayyana fatan cewa wata rana gaskiya ta yi halintama gano hakikanin musabbabin mutuwar Dele Giwa.

Ya bayyana takaici cewa ’yan jarida sun kawo koma baya  ga binciken kisan, inda suka yi saurin yanke hukunci kafin a kammala binciken.

A cewarsa, ya yi fatan a lokacin da gwamantin farar hula ta Olusegun Obasanjo ta sake buɗe binciken kisan Dele Giwa ’yan sanda za su samo sabbin hujjoji da ke nuna abin da ya faru, amma hakan bai samu ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dele Giwa kisan Dele Giwa

এছাড়াও পড়ুন:

An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m

Rundunar ’yan sandan Jihar Borno ta raba zunzurutun kuɗi naira miliyan 63.4 ga iyalan jami’anta 84 da suka rasa rayukansu a bakin aiki.

Rundunar ta raba kudin ne a ƙarƙashin tsarin inshorar rayuwa da kuma tsarin kula da lafiyar iyali na Sufeto Janar na ’yan sanda.

 

An gudanar da rabon kuɗin ne a ranar Alhamis a Maiduguri babban birnin jihar kamar yadda Kakakin rundunar a jihar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya bayyana a cikin wata sanarwa.

A cewar sanarwar, Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, CP Naziru Abdulmajid, wanda ya wakilci Sufeto Janar na ‘yan sanda, IGP Kayode Egbetokun, shi ne ya gabatar da takardun cakin kudin ga iyalan waɗanda suka ci gajiyar tallafin.

“Harkokin da suka shafi jami’anmu da iyalansu ya kasance babban fifiko ga rundunar,” in ji CP Abdulmajid yayin taron.

Ya ce wannan shiri na nuna tausayi da rikon amana, da kuma jagoranci mai nagarta daga Sufeto Janar wajen girmama jaruman da suka sadaukar da rayukansu domin tabbatar da zaman lafiya da tsaron ƙasa.

Kwamishinan ya kuma yi kira ga iyalan da suka amfana da tallafin da su yi amfani da kuɗaɗen yadda ya dace, musamman wajen tallafa wa ilimi, kiwon lafiya, da jin daɗin rayuwar iyalansu gaba ɗaya.

Ya yaba wa Sufeto Janar bisa ci gaba da tsare-tsaren jin daɗin jami’an rundunar, yana mai bayyana su a matsayin muhimman hanyoyin da ke samar da agaji da kwanciyar hankali ga iyalan waɗanda suka rasa masoyansu.

A nata jawabin a madadin iyalan da suka amfana, Misis Nana Goni ta nuna godiya ga Sufeto Janar bisa goyon bayan da ya bayar, tana mai tabbatar da cewa za su yi amfani da kuɗaɗen yadda ya kamata don inganta rayuwar iyalansu.

Rundunar ta bayyana cewa wannan rabon tallafi ya sake tabbatar da jajircewarta wajen kula da walwala da mutuncin jami’anta da iyalansu, musamman waɗanda suka sadaukar da rayukansu wajen kare al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka
  • Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Amurka ta sanya Najeriya cikin ƙasashen da ake yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida
  • An raba wa iyalan jami’an ’yan sandan da suka rasu a bakin aiki a Borno N63.4m
  • Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar  Christopher Musa