Ba ni da hannu a kisan Dele Giwa — Janar Babangida
Published: 21st, February 2025 GMT
Tsohon shugaban kasa na mulkin soja, Janar Ibrahim Badamasi Babangida ta nesanta hannunsa da kisan gogaggen ɗan jarida kuma Babban Editan Jaridar Newawatch, Dele Giwa.
An kashe Dele Giwa wanda fitaccen mai sukar gwamnatin Babangida ne, ta hanyar wasikar bom a gidansa da ke Legas a ranar 19 ga watan Oktoban 1986.
Kwana biyu kafin kisan nasa wani babban jami’in Rundunar Leƙen Asiri ta Soji ya zargi Dele Giwa da yin fasa-kwaurin makamai da ƙasashen da nufin tayar da zaune tsaye a Najeriya
Sakamakon haka, dan jaridar ya yi hanzarin sanar da lauyansa, Gani Fawehinmi, game da halin da ake ciki.
Na yi nadamar soke zaɓen 1993 — Babangida NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ba Za Mu Sauke Farashin Burodi Ba —’Yan kasuwaAmma bayan kwanan biyu, wani babban hafsan soji, Kamar Halilu Akilu, ya kira waya ta ba Dele Giwa tabbacin cewa kuskure aka samu kuma an gano ainihin lamarin, don haka ya kwantar da hankalinsa, komai ya wuce.
Wani abokin Dele Giwa a Newawatch mai suna Ray Ekpu, ya ce bayan ’yan sa’o’i ne aka kai wani sako gwamnati gidan Dele Giwa.
Ray Ekpu ya bayyana cewa ɗan Dele Giwa mai suna Billy ne ya karbi sakon mai ɗauke da tambarin Fadar Shugaban Ƙasar ya mika wa mahaifin nasa, wanda a lokacin yake cin abinci tare da wakilin Newawatch na London, Kayode Soyinka, wand ya kawo mishi ziyara.
Wasikar mai ɗauke da tambarin Fadar Shugaban Ƙasa na kuma dauke da rubutun “wanda aka aika wa kaɗai zai buɗe.”
Amma a yanzu shekara 41 bayan kisan na Dele, Janar Babangida ya nesanta hannunsa ko masaniyar lamarin.
Babangida ya nesanta kansa da lamarin ne a littafin Tarihi da da ya ƙaddamar a ranar Alhamis a Abuja.
Babangida ya bayyana fatan cewa wata rana gaskiya ta yi halintama gano hakikanin musabbabin mutuwar Dele Giwa.
Ya bayyana takaici cewa ’yan jarida sun kawo koma baya ga binciken kisan, inda suka yi saurin yanke hukunci kafin a kammala binciken.
A cewarsa, ya yi fatan a lokacin da gwamantin farar hula ta Olusegun Obasanjo ta sake buɗe binciken kisan Dele Giwa ’yan sanda za su samo sabbin hujjoji da ke nuna abin da ya faru, amma hakan bai samu ba.উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dele Giwa kisan Dele Giwa
এছাড়াও পড়ুন:
Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027
’Yan siyasar yankin Arewa na ganin dole sai da goyon bayansu ɗan takara zai yi nasara a zaben Shugaban ƙasa.
Hakan na zuwa ne bayan tsohon maitaimaka wa shugaban ƙasa a fannin siyasa, Alhaji Hakeem Baba-Ahmed ya yi wata hira, inda yake cewa, nan da wata shida yankin zai fitar da matsayarsa.
An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APCDuk da cewa Hakeem ba shi ne mai magana da yawun al’ummar yankin ba, amma ana kallon sa a matsayin daya daga cikin manya a yankin, saboda tsohon matsayinsa na mai magana da yawun Kungiyar Dattawan Arewa (NEF).
Tsarin siyasar kasar nan ya sa dole ne kowane dan takara ya zaga kowane lungu da sako na kasar nan kafin ya iya samun kuri’un da yake bukata don ya samu nasara.
Masana harkokin siyasa na ganin kalaman na Hakeem da ire-irensa na kan hanya, amma idan aka cika sharadi daya kacal.
“Rawar da Arewa za ta taka a zaben 2027 ba ta da wani bambanci da wadda ta saba takawa, kuma hakan zai yiwu ne kawai idan ta ci gaba da zama dunkulalliya, mai alkibla daya,” in ji Malam Kabiru Sufi na Kwalejin Share Fagen Shiga Jami’a ta Jihar Kano.
Idan dai aka cika wannan sharaɗi, to duk wani ɗan takara ko datn Arewa ne sai ya nemi goyon bayan ‘yan Arewacin kafin ya yi nasara.
Ya bayar da misalin haɗakar da jam’iyyun siyasa suka yi kafin babban zaben 2015, inda jam’iyyun CPC da ACN da ANPP da wani ɓangare na APGA da wasu gwamnonin PDP suka kafa APC mai mulkin.
“Idan aka samu rarrabuwar kai kuma, to Arewa za ta zama kamar wani taron tsintsiya ne ba shara. Babu rawar da za ta taka”, in ji Sufi.
Malam Sufi ya ce ɗaya daga cikin dalilan da suka sa ‘yan Arewa ke jin cewa sai da su za a ci zaɓe shi ne yawan al’umma.
A zaɓen 2023 da ya gabata, sahihan kuri’un da ‘yan takara huɗun farko suka samu a jihohin Arewa sun zarta na Kudu da kusan miliyan biyar.
Bola Ahmed Tinubu na Jam’iyyar APC da Alhaji Atiku Abubakar na PDP da Mista Peter Obi na LP da Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso na NNPP, sun samu jimillar kuri’u miliyan 13,716,667 a jihohin Arewa. Sun samu jimillar 9,020,741 a jihohin Kudu.
Bola Tinubu da ya lashe zaɓen ya samu jimillar 5,346,404 a jihohin Arewa, yayin da ya samu 3,206,969 a jihohin Kudu.
“In dai Arewa ta sake yin abin da ta yi a 2015, tabbas dole ne sai an nemi goyon bayanta, amma idan aka samu rarrabuwar kai za ta zama mushen gizaka – ana yi mata kallon za ta iya, amma kuma ba za ta iya ba,” kamar yadda Sufi ya bayyana.
Shin ko Arewan za ta iya magana da murya ɗaya?
Farfesa Abubakar Ma’azu, masanin harkokin siyasa ne a Jami’ar Maiduguri yana ganin za ta iya yin hakan.
“Idan aka duba, wadanda suka kafa Jam’iyyar APC sun fara yunkurin ne tun a 2011.
“Abin bai yiwu ba, amma suka shiga zabe a haka kuma suka sha kaye. Sai daga baya suka gano kuskurensu kuma suka yi nasara a 2015 bayan cim ma hadakar,” in ji shi.
Ko zai yiwu a iya cin zabe da kuri’un Arewa kawai? Kamar yadda ’yan Arewa ke tutiya da cewa sai da goyon bayansu za a ci zaɓen Shugaban ƙasa, haka ma sai dan takara ya samu kuri’u a Kudanci kafin ya yi nasara.
Kafin hadakar APC ta kayar da PDP mai mulki, tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi takara har sau uku ba tare da nasara ba, har sai bayan da ya samu goyon bayan wasu jam’iyyu daga Kudu.
Buhari ya fara yin takara ce a Jam’iyyar APP a 2003, ya sake yi a 2007 a jam’iyyar bayan ta zama ANPP, sai a 2011 kuma ya yi a CPC.
Ana ganin shigar Jam’iyyar ACN ta Bola Tinubu cikin haɗakar APC ce ƙashin bayan nasarar Buhari, saboda yadda take da tasiri a jihohin Kudu maso Yamma da Yarabawa ke da rinjaye.
Kazalika, Atiku Abubakar na Jam’iyyar PDP a zaben 2023 ya samu kuri’u mafiya yawa a Arewaci (4,834,767) sama da kudanci (1,751,047), amma duk da haka bai yi nasara ba.
“Dole ne sai ɗan takara ya karaɗe ƙasa baki ɗaya, ya samu kuri’u a Kudu da Arewa kafin ya samu kowace irin nasara,” in ji Farfesa Ma’azu.