Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
Published: 20th, February 2025 GMT
Shugaban kasar na Amurka Donald Trump ya wallafa wani sako a shafinsa na “Truth Social” da a ciki ya bayyana Volodymyr Zelenskyy dad an kama-karya, kuma abinda ya fi yi masa alheri shi ne ya yi wani abu da sauri, domin idan ba haka ba,zai yi asarar kasarsa baki daya.
Shugaban na kasar Amurka ya kara da cewa; Volodymyr Zelenskyy ya sa Amurka ta kashe dala biliyan 350 da ya shiga cikin yakin da ba zai iya samun nasara ba.
Har ila yau, shugaban na Amurka ya ce, shi kanshi Volodymyr Zelenskyy ya yi furuci da cewa, rabin kudaden da mu ka aika masa sun bace, kuma ya ki gudanar da yin zabe, don haka masu goyon bayansa ‘yan kadan ne.”
Bugu da kari Trump ya ce, ko kadan bai kamata a ce yaki ya barke ba, domin yaki ne da babu yadda za a yi ya yi nasara ba tare da goyon bayan Amurka da kuma Trump ba, yana mai yin ishara da cewa, ahalin yanzu Amurka tana tattaunawa cikin nasara da Rasha domin kawo karshen yakin.”
Wani sashe na sakon Trump din ya kunshi cewa; Ina son kasar Ukiraniya, sai dai abinda Volodymyr Zelenskyy ya yi, ya munana, ya ruguza kasarsa, kuma miliyoyin mutane sun mutu ba tare da dalili ba.
A gefe daya, kasashen turai sun mayar da martani akan maganganun na Trump, inda shugaban gwamantin Jamus ya ce shugaban kasar ta Ukiraniya ba dan dan kama-karya ba ne.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Matar aure ta yanka wuyan mijinta, ta fasa masa ido da wuƙa a Neja
An kama wata matar aure a garin Kuta, hedikwatar Karamar Hukumar Shiroro ta Jihar Neja, bisa zargin yankar wuyan mijinta, Salisu Suleiman, da wukar girki.
Majiyoyi sun ce matar ta kuma soka wa mijin wuka a idonsa na hagu, lamarin da ya lalata idon gaba ɗaya.
Wata majiya da ta nemi a ɓoye sunanta ta bayyana wa wakilinmu cewa ma’auratan sun samu saɓani ne, inda matar ta jira har sai da mijin ya kwanta barci kafin ta kai masa hari da wuƙa.
Kakakin ’yan sanda na Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya ce lamarinya auku ne da safiyar Asabar, 1 ga Nuwamba, 2025.
A cewarsa, “A ranar 1 ga Nuwamba, da misalin ƙarfe 2:30 na asuba, wani Salisu Suleiman na garin Kuta ya samu saɓani da matarsa, Halima Salisu, inda da mijin ya kwanta barci, matar ta ɗauki wuƙa ta yankar masa wuya, sannan ta soka masa a idon hagu.”
SP Abiodun ya ce an garzaya da wanda abin ya faru da shi Asibitin Gabaɗaya na Kuta, daga nan kuma aka mayar da shi Asibitin Ƙwararru na IBB da ke Minna domin ƙarin kulawar likitoci.
Ya ƙara da cewa, “An kama wadda ake zargi, kuma tana tsare a hannun ’yan sanda domin ci gaba da bincike da kuma gurfanar da ita a gaban kotu.”