Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno
Published: 19th, February 2025 GMT
Aƙalla mutum 11 sun shaƙi iskar ’yanci bayan kuɓuta daga hannun ƙungiyar mayaƙan Boko Haram masu iƙirarin jihadi a Jihar Borno.
Waɗanda suka shaƙi iskar ’yancin na daga cikin mutanen da ƙungiyar Boko Haram ta sace a wani wurin kamun kifi a Doron Baga.
Majalisar Edo ta tanadi hukuncin kisa kan masu garkuwa da mutane USAID: Amurka za ta yi bincike kan ɗaukar nauyin Boko HaramWata majiya ta bayyana cewa, wani kwamandan ’yan ta’addan mai suna Tar ne ya jagoranci garkuwa da mutanen ne a ranar 13 ga watan Fabrairu 2025.
Tar da tawagarsa da ke addabar masunta da manoma a gaɓar Tafkin Chadi sun ɗauke mutanen ne yayin da suka afka wa al’ummar Shawaram da ke ƙarƙashin Ƙaramar Hukumar Kukawa ta jihar, inda suka yi awon gaba da mutane 14 da suka haɗa da mata da ƙananan yara.
Wani shugaban al’ummar yankin da ya nemi a sakaya sunansa ya bayyana cewa ’yan ta’addan sun nemi kuɗin fansa jim kaɗan bayan sace su.
Ya bayyana cewa an ceto mutane 11 bayan an biya kuɗin fansa na Naira miliyan 1.4 da wasu al’umma suka tara.
A cewarsa, har yanzu akwai mutane uku da ake garkuwa da su —ciki har da mace guda mahaifinta — a hannun ’yan ta’addan.
Majiyar ta ce mace ta zaɓi ci gaba da zama a hannun ’yan ta’addan saboda sun ƙi sakin mahaifin nata.
Majiyar ta ƙara da cewa Tar ya gindaya sharaɗin cewa muddin ba a biya musu buƙatar sako ragowar mutanen uku ba, zai aurar da macen da ke cikinsu tare da ɗaukar hukunci mai tsanani kan sauran waɗanda ke hannunsa.
Sai dai har zuwa yanzu mahukuntan da wakilinmu ya tuntuɓa ba su ce komai dangane da lamarin ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram jihar Borno yan ta addan
এছাড়াও পড়ুন:
Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara
Yarjejeniyar, a cewar daukacin mahalarta taron, ta nuna wani gagarumin mataki na kawo karshen tashe-tashen hankula, garkuwa da mutane da satar shanu a Arewa maso Yamma, da kuma yankin Arewa.
Yarjejeniyar wacce Mai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi, da shugaban karamar hukumar, Babangida Abdullahi Kurfi suka shirya, ta gudana ne a dajin Wurma, inda ake fama da rashin tsaro.
Manyan jagororin ‘yan bindigan da suka hada da Alhaji Usman Kachalla Ruga da Sani Muhindinge da Yahaya Sani (Hayyu) da kuma Alhaji Shu’aibu duk sun yi alkawarin tsagaita wuta.
Daga baya suka sako mutanen da suka kama kuma suka bar manoma su koma gonakansu ba tare da wata barazana ba.
Sai dai kasa da wata guda da kulla yarjejeniyar, an tattaro cewa ‘yan bindigar sun sake kai hari a Zamfara inda suka yi awon gaba da masallata da dama.
Wata majiya ta cikin garin, ta shaida cewa, harin ya afku ne a lokacin sallar asuba da misalin karfe 5:30 na safe, inda ‘yan bindigar suka afkawa masallacin, suka kewaye shi, sannan suka tattara masallatan zuwa daji.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp