Aminiya:
2025-06-15@12:47:29 GMT

Yadda USAID ke ɗaukar nauyin Boko Haram —Dan Majalisar Amurka

Published: 14th, February 2025 GMT

Dan Majalisar Dokokin Amurka, Scott Perry, ya yi ikirarin cewa Hukumar Raya Kasashe ta Amurka (USAID) ce ke ɗaukar nauyin kungiyoyin ta’addanci ciki har da Boko Haram.

Perry, dan jam’iyyar Republican mai wakiltar Pennsylvania, ya yi wannan ikirarin ne a taron sauraron sauraron ra’ayin na karamin kwamiti kan ingancin gwamnati a ranar Alhamis.

Kungiyar Boko Haram ta shafe sama da shekaru 15 tana kai hare-hare ayankin Arewa maso Gabashin Najeriya, inda ta kashe dubun-dubatar jama’a, ciki har da  ‘yan sanda, da sojoji da fararen hula.

Hare-haren kungiyar sun yi sanadin mutuwar yara fiye da 300,000, da raba mutun miliyan 2.3 da gidajensu da kuma haifar da matsalar abinci da yunwa a yankin.

A yayin zaman wanda ya mayar da hankali kan zargin karkatar da kudaden, Perry ya ce kuɗaɗen masu biyan haraji, “Dala miliyan 697 a duk shekara USAID krnkashewa, da kuma safarar kudaden kudade kungiyoyin ISIS da Al-Qaeda da Boko Haram da ISIS Khorasan, da kuma sansanonin horar da ’yan ta’adda.”

Ya kuma ce hukumar ta USAID ta bayar da dala miliyan 136 don gina makarantu 120 a Pakistan, inda ya yi zargin wata shaida ko da ke nuna gina makarantun.

Shugaba Donald Trump ya bayar da umarnin rufe hukumar ta USAID, kan zargin ta da cin hanci da rashawa a wani sako da ya wallafa.

Shi ma Elon Musk, abokin Trump, kuma shugaban ma’aikatar kula da ayyukan gwamnati, ya soki hukumar ta USAID, yana mai zargin cewa tana gudanar da ayyukan damfara.

Daga cikin wasu sukar, Musk ya yi iƙirarin cewa USAID tana “aikin leƙen asiri kamar CIA” har ma da “binciken kuɗaɗen binciken makaman ƙare-dangi, gami da COVID-19, wanda ya kashe miliyoyin mutane.”

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2

Abdulazeez pleaded not guilty to the two-count charge. Abdulazeez ya ki amsa laifin da ake tuhumarsa da su biyu.

Bayan rokon da ta yi, lauyan ICPC, Hamza Sani, ya bukaci kotun ta dage sauraron karar zuwa ranar 13 ga watan Yuni, 2025, domin masu gabatar da kara su gabatar da shaidu.

Sai dai daga baya kotun ta ba da ranar sannan ta dage sauraron karar zuwa ranar 20 ga watan Yunin 2025 domin sauraron karar.

Lauyan wanda ake tuhuma ya nemi a ba shi belin, wanda ICPC ba ta yi adawa da shi ba.

Mai shari’a Iheabunke ya bayar da belinta a kan kudi naira miliyan 10, tare da mutane biyu da za su tsaya mata.

Ya ce dole ne wadanda ake kara su mallaki kadarorin da ke karkashin ikon kotun, sannan su mika takardun mallakar asali ga magatakardar kotun don tantancewa, sannan wanda ake kara ya sanar da kotu a hukumance kafin tafiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka
  • ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2