Gwamnatin Tinubu ba za ta hana ni magana ba — Farfesa Yusuf
Published: 13th, February 2025 GMT
Tsohon Shugaban Hukumar Inshorar Lafiya ta Ƙasa (NHIS), Farfesa Usman Yusuf, ya zargi Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da ƙoƙarin hana shi magana sakamakon sukar manufofinta da yake yi.
Yusuf, wanda ya yi ƙaurin suna wajen sukar gwamnati, Hukumar EFCC ta kama shi tare da gurfanar da shi a kotu bisa zargin rashawa.
Sai dai ya musanta dukkanin zarge-zargen, inda ya ce an shirya masa tuggu ne saboda dalilan siyasa.
Da yake magana yayin da yake tsare a gidan gyaran hali na Kuje, ya ce, “Wannan wani yunƙuri ne na hana ni yin magana kawai. Zarge-zargen EFCC ba su da tushe balle makama, kuma suna amfani da tsoffin maganganu marasa tushe.
“Ina da ƙwarin gwiwa cewa lauyoyina za su kare ni.”
Farfesa Yusuf ya kuma zargi jami’an tsaro da bibiyarsa da iyalansa.
“Tun tsawon watanni suke bin diddigin rayuwata, a zahiri da kafafen sada zumunta.
“Wannan gwamnati na amfani da hanyoyin danniya domin hana jama’a faɗin albarkacin bakinsu, kamar yadda aka saba a zamanin mulkin soja,” in ji shi.
Kama shi ya jawo ce-ce-ku-ce daga ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam da kuma ’yan adawa, waɗanda suka bayyana hakan a matsayin yunƙurin muƙushe ’yancin faɗin albarkacin baki.
Wasu masu rajin kare haƙƙin ɗan Adam, sun buƙaci a saki Yusuf nan take, inda suka ce suka da adawa ga manufofin gwamnati bai kamata a ɗauke su a matsayin laifi ba.
“Dimokuraɗiyya na buƙatar ra’ayoyi mabambanta. Amfani da tsoratarwa da shari’a don hana masu suka magana babbar barazana ce ga ’yancin jama’a,” in ji wani mai rajin kare haƙƙin ɗan Adam.
Duk da kasancewarsa a tsare, Yusuf ya yi alƙawarin ci gaba da magana kan yadda gwamnatin Tinubu ta gaza.
Ya buƙaci ’yan Najeriya da su zama masu lura da kuma neman haƙƙinsu a wajen gwamnati.
“Wannan ba batuna ne ni kaɗai ba. Batun kare ’yancin jama’a ne da hana kowace gwamnati amfani da tsoro don muƙushe al’umma.
“Dole mu tashi tsaye don kare haƙƙoƙinmu,” in ji shi.
Yanzu haka dai yana tsare yayin da kotu ta ɗage zaman sauraron buƙatar bayar da belinsa zuwa ranar 27 ga watan Fabrairu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Farfesa Usman Yusuf gwamnati
এছাড়াও পড়ুন:
Ina Fatan Cigaba Da Taka Leda Har Zuwa Lokacin da Zan Cika Shekara 40 A Duniya – Salah
Da yake magana da tashar talabijin ta ON Sports, Salah ya ce “Zan daina wasa ne kawai idan na fara jin gajiya a jikina”, “Idan ka tambaye ni ra’ayi na, ina tsammanin zan iya taka leda har zuwa shekaru 39 zuwa 40 amma idan na ji ina so in daina, zan daina, na samu abubuwa da yawa a harkar kwallon kafa”, inji Salah wanda ya lashe kyautar gwarzon dan wasan Firimiya Lig ta bana.
Salah ya ci wa Liverpool da Chelsea kwallaye 186 a gasar firimiya kuma ya na matsayi na biyar a jerin wadanda suka fi kowa zura kwallo a raga inda kwallo daya kacal ta rage ya cimma tsohon dan wasan Newcastle da Manchester United Andrew Cole, dan wasan na Masar ya nuna cewa zai iya taka leda a Gabas ta Tsakiya bayan kwantiraginsa a Anfield ya kare a shekara ta 2027.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp