Gwamnatin Tinubu ba za ta hana ni magana ba — Farfesa Yusuf
Published: 13th, February 2025 GMT
Tsohon Shugaban Hukumar Inshorar Lafiya ta Ƙasa (NHIS), Farfesa Usman Yusuf, ya zargi Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da ƙoƙarin hana shi magana sakamakon sukar manufofinta da yake yi.
Yusuf, wanda ya yi ƙaurin suna wajen sukar gwamnati, Hukumar EFCC ta kama shi tare da gurfanar da shi a kotu bisa zargin rashawa.
Sai dai ya musanta dukkanin zarge-zargen, inda ya ce an shirya masa tuggu ne saboda dalilan siyasa.
Da yake magana yayin da yake tsare a gidan gyaran hali na Kuje, ya ce, “Wannan wani yunƙuri ne na hana ni yin magana kawai. Zarge-zargen EFCC ba su da tushe balle makama, kuma suna amfani da tsoffin maganganu marasa tushe.
“Ina da ƙwarin gwiwa cewa lauyoyina za su kare ni.”
Farfesa Yusuf ya kuma zargi jami’an tsaro da bibiyarsa da iyalansa.
“Tun tsawon watanni suke bin diddigin rayuwata, a zahiri da kafafen sada zumunta.
“Wannan gwamnati na amfani da hanyoyin danniya domin hana jama’a faɗin albarkacin bakinsu, kamar yadda aka saba a zamanin mulkin soja,” in ji shi.
Kama shi ya jawo ce-ce-ku-ce daga ƙungiyoyin kare haƙƙin ɗan Adam da kuma ’yan adawa, waɗanda suka bayyana hakan a matsayin yunƙurin muƙushe ’yancin faɗin albarkacin baki.
Wasu masu rajin kare haƙƙin ɗan Adam, sun buƙaci a saki Yusuf nan take, inda suka ce suka da adawa ga manufofin gwamnati bai kamata a ɗauke su a matsayin laifi ba.
“Dimokuraɗiyya na buƙatar ra’ayoyi mabambanta. Amfani da tsoratarwa da shari’a don hana masu suka magana babbar barazana ce ga ’yancin jama’a,” in ji wani mai rajin kare haƙƙin ɗan Adam.
Duk da kasancewarsa a tsare, Yusuf ya yi alƙawarin ci gaba da magana kan yadda gwamnatin Tinubu ta gaza.
Ya buƙaci ’yan Najeriya da su zama masu lura da kuma neman haƙƙinsu a wajen gwamnati.
“Wannan ba batuna ne ni kaɗai ba. Batun kare ’yancin jama’a ne da hana kowace gwamnati amfani da tsoro don muƙushe al’umma.
“Dole mu tashi tsaye don kare haƙƙoƙinmu,” in ji shi.
Yanzu haka dai yana tsare yayin da kotu ta ɗage zaman sauraron buƙatar bayar da belinsa zuwa ranar 27 ga watan Fabrairu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Farfesa Usman Yusuf gwamnati
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
Gwamnatin Jihar Yobe ta ƙaddamar da shirin fara amfani da ma’adinan ƙarƙashin ƙasa da Allah SWT ya hore ma ta da nufin haɓaka tattalin arzikinta tare da samarwa al’umma aikin yi.
A yayin ƙaddamar da taron masu ruwa da tsaki na Jihar da aka yi a babban ɗakin taron gidan gwamnatin Jihar da ke Damaturu, Gwamnan Jihar Mai Mala Buni ya ce kamfanin haɓaka ma’adanai ta Yobe Limited ita ce kawai hukumar da aka bai wa izini don gudanar da duk ayyukan bincike da haƙar ma’adinai a faɗin jihar.
Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFAYana mai cewa, kamfanin haƙar ma’adinai na Yobe a halin yanzu shi ne, ƙashin bayan da zai samarwa Jihar hanyoyin dogaro.
“Jihar Yobe tana da wadataccen albarkatun ma’adinai kamar: Limestone, gypsum, kaolin, granite, Quartz, silica da sauran su duk da haka, tsawon shekaru da yawa, waɗannan ma’adinai sun kasance ba a amfani da su sosai kuma a yanzu lokaci ya yi da za a mayar da waɗannan ma’adinai da aka ɓoye zuwa kadarorin da za su samar da ayyukan yi, samar da wadata da kuma ciyar da ci gaban zamantakewa da tattalin arziki na mutanenmu gaba ɗaya.”
“Manufarmu ita ce tsara wani tsari don ci gaban fannin haƙar ma’adinai a Jihar Yobe ta hanyar da ta dace da manufofin Gwamnatin Tarayya na tabbatar da haɗa kan al’umma, jawo hankalin masu zuba jari masu aminci da kuma tabbatar da alhakin gyara muhalli.
“kuma mun yi imanin cewa haƙar ma’adinai idan aka sarrafa shi yadda ya kamata, zai iya zama babban abin da ke haifar da juriyar tattalin arzikin jiharmu, samar da aikin yi ga matasa da kuma samar da kuɗaɗen shiga.”
“Muna hasashen samar da fannin haƙar ma’adinai wanda zai iya aiki a cikin tsarin dokoki, wanda ke tabbatar da ɗorewar muhalli da fa’idar al’umma; wanda ke haɗaka da haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu waɗanda aka amince da riƙon amana; wanda ke jawo hankalin masu zuba jari na ƙasashen waje.” Cewar Gwamna Buni.