Aminiya:
2025-05-01@04:16:11 GMT

NHIS: Kotu ta ɗage bayar da belin Farfesa Yusuf zuwa 27 ga Fabrairu

Published: 13th, February 2025 GMT

Wata Babbar Kotu a Abuja, ta ɗage yanke hukunci kan buƙatar bayar da belin Tsohon Shugaban Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Ƙasa (NHIS), Farfesa Usman Yusuf, wanda ke fuskantar zargin cin hanci da rashawa.

A ranar Laraba ne, Mai shari’a Chinyere Nwecheonwu, ta bayar da umarnin ci gaba da tsare Yusuf a gidan gyaran hali na Kuje har zuwa ranar 27 ga watan Fabrairu.

Sojoji sun doki ’yan sanda kan kama ‘mai laifi’ Fitaccen ɗan siyasa Ahmadu Haruna Zago ya rasu

A lokacin ne kotun za ta yanke hukunci kan buƙatar bayar da belinsa.

Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC), na zargin Yusuf da karkatar da kuɗaɗen gwamnati lokacin da yake jagorancin NHIS a shekarar 2016.

Ana zargin ya amince da sayen mota kan kuɗi Naira miliyan 49.2 maimakon Naira miliyan 30 da aka ware a kasafin kuɗi.

Hakazalika, EFCC ta ce Yusuf ya bai wa gidauniyar GK Kanki Foundation kwangilar bayar da horo ta Naira miliyan 10.1ba tare da bin ƙa’ida ba, duk da cewa mutum 45 kaɗai aka horar maimakon 90 da aka bayyana.

Bugu da ƙari, ana tuhumarsa da bai wa kamfanin ɗan uwansa Hassan Yusuf, Lubekh Nigeria Limited kwangilar Naira miliyan 17.5, wadda ita ma aka ce ba bisa ƙa’ida aka yi ta ba.

Yusuf ya musanta duk zarge-zargen da ake yi masa.

A zaman kotun, lauya mai gabatar da ƙara, Francis Usani, ya buƙaci a hana belin Yusuf, inda ya ce bai cika sharuɗan belin da EFCC ta ba shi a baya ba, wanda ya haɗa da wajibcin kai kansa ofishin hukumar sau biyu a kowane mako.

Ya ƙara da cewa Yusuf ya yi fariya da dangantakarsa da masu ruwa da tsaki a siyasa, don haka akwai yiwuwar ya tsere idan aka bayar da belinsa.

Ya kuma bayyana cewa jami’an EFCC sun sha wahala kafin su kama shi tare da gurfanar da shi a kotu.

Sai dai lauyan Yusuf, O.I. Habeeb (SAN), ya roƙi kotu da ta bayar da belinsa, inda ya ce laifukan da ake zargin sa da suna da ikon samun beli bisa doka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Farfesa Usman Yusuf zargi bayar da belin Naira miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Fagen siyasar Najeriya na ci gaba da jijjiga sakamakon sauya sheƙar da ’yan siyasa daga ɓangarori daban-daban suke yi.

A baya-bayan nan tsallakawar da wasu jiga-jigan jam’iyyun adawa suka yi zuwa Jam’iyyar APC mai mulki ta jawo ɗiga ayar tambaya a kan dalilansu da kuma makomar hamayya a zaɓen 2027.

Hakan dai yana faruwa ne a daidai lokacin da wasu ’yan ƙasar suke kokawa bisa yadda ake gudanar da mulki da kuma yadda wasu manyan ’yan siyasa suke fadi-tashin kafa wata inuwa da suka ce za ta ciro wa talaka kitse a wuta ta hanyar kawar da gwamnatin APC.

NAJERIYA A YAU: Dalilin da zazzaɓin cizon sauro ba ya jin magani DAGA LARABA: Dalilan Rashin Wutar Lantarki A Wasu Jihohin Arewa

Wannan shi ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai da nufin gano alƙiblar da siyasar Najeriya take shirin fuskanta.

Domin sauke shirin. Latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
  • Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato 
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine
  • Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi
  • NAJERIYA A YAU: “Dalilin da muke sauya sheƙa zuwa jam’iyya mai mulki”