HausaTv:
2025-11-03@11:02:35 GMT

HKI: Barazana Ba Ta Tasiri Akan Hamas

Published: 11th, February 2025 GMT

Kafafen watsa labarun HKI sun ce; Barazanar da ake yi wa kungiyar Hamas ba ta wani tasiri a gare ta.

Kafafen watsa labarun na HKI suna yin tambaya akan yadda Hamas din take isar da sakwanni a fakaice ga Isra’ila a yayin bikin mika fursunoni da take shiryawa.

Tashar talabijin din ta 12: ta ambaci cewa; A cikin wannan yanayi mai tsanani da ake ciki, ko wane sako ne kungiyar ta Hamas take son isarwa ta hanyar shirya biki a yayin sakin fursunoni?

Shi kuwa mai yi tashar sharhi, Ohad Hamu, ya ce kungiyar ta Hamas ta isar da sako da harshen Hebrew da take mahana da Isra’ilawa, sai kuma turanci da take Magana da gwamnatin Amurka, da hakan yake nufin kin amincewa da shirin Donald Trump.

Ita kuwa tashar talabijin ta 13: cewa ta yi  Hamas ta yi watsi da dukkanin  sakwannin  da Isra’ila  take aike mata, kuma ko kadan ba ta damu da barazanar da ake yi ma ta ba.

Har ila yau tashar talabijin ta 12; ta ce, hotonnin da suke fitowa daga Gaza suna nuni da cewa, har yanzu Hamas ce take iko da yankin.

Shi kuma tsohon Fira ministan HKI Ehud Barack cewa ya yi; rashin tsayyar manufa ta gwmanatin Netanyahu ne ya sa har yanzu Hamas din yake ci gaba da iko da Gaza. Ya kuma kara da cewa, ba ta hanyar kashe shugabannin Hamas ne za a kawo karshenta ba, sai dai ta hanyar samar da wadanda za su maye gurbinta.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza

Gwamnatin mamayar Isra’ila ta yanke hukuncin kisa kan masu fama da cutar kansa da kuma waɗanda suke fama da matsalar koda na mutuwa a Gaza domin hana fitar da su wata kasa don neman magani

Cibiyar Kare Hakkin Dan Adam ta Gaza ta bayyana matukar damuwarta game da tabarbarewar lafiyar marasa lafiya da ke fama da cutar kansa da kuma cutar koda a Zirin Gaza. Wadannan cututtuka sun kara ta’azzara ne sakamakon hare-haren sojojin mamayar Isra’ila kan Gaza da kuma ci gaba da killace yankin bayan tsagaita bude wuta, gami da hana shigar dq magunguna da kayayyakin ayyukan likitanci masu muhimmanci cikin yankin. Cibiyar ta kuma yi nuni da tsauraran matakan fitar da marasa lafiya zuwa ƙasashen waje don neman magani.

A cikin wata sanarwa da aka fitar a ranar Lahadi, Cibiyar ta tabbatar da cewa, wannan yanayin ba shi da wata shakka cewa Isra’ila na aiwatar da manufar kisan gilla a kan dubban marasa lafiya ta hanyar hana su ‘yancinsu na rayuwa da magani da gangan, da kuma canza wahalarsu zuwa wani nau’in hukunci na gama gari.

Cibiyar ta ambaci majiyoyin lafiya da ke tabbatar da cewa, akwai marasa lafiya 12,500 da ke fama da cutar kansa a Zirin Gaza, ciki har da ƙananan yara. Ta lura cewa mata sun kai kusan kashi 52% na dukkan masu cutar kansa a Gaza.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas Ta yi Watsi Da Zargin Da Amurka Tayi Mata Kan Batun Motocin Agaji A Gaza
  • Al’ummar Kauru Sun Koka Game Da Karuwar Hare-hare Da Ke Barazana Ga Gonaki Da Rayuka
  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
  • Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu