HausaTv:
2025-06-16@00:31:13 GMT

HKI: Barazana Ba Ta Tasiri Akan Hamas

Published: 11th, February 2025 GMT

Kafafen watsa labarun HKI sun ce; Barazanar da ake yi wa kungiyar Hamas ba ta wani tasiri a gare ta.

Kafafen watsa labarun na HKI suna yin tambaya akan yadda Hamas din take isar da sakwanni a fakaice ga Isra’ila a yayin bikin mika fursunoni da take shiryawa.

Tashar talabijin din ta 12: ta ambaci cewa; A cikin wannan yanayi mai tsanani da ake ciki, ko wane sako ne kungiyar ta Hamas take son isarwa ta hanyar shirya biki a yayin sakin fursunoni?

Shi kuwa mai yi tashar sharhi, Ohad Hamu, ya ce kungiyar ta Hamas ta isar da sako da harshen Hebrew da take mahana da Isra’ilawa, sai kuma turanci da take Magana da gwamnatin Amurka, da hakan yake nufin kin amincewa da shirin Donald Trump.

Ita kuwa tashar talabijin ta 13: cewa ta yi  Hamas ta yi watsi da dukkanin  sakwannin  da Isra’ila  take aike mata, kuma ko kadan ba ta damu da barazanar da ake yi ma ta ba.

Har ila yau tashar talabijin ta 12; ta ce, hotonnin da suke fitowa daga Gaza suna nuni da cewa, har yanzu Hamas ce take iko da yankin.

Shi kuma tsohon Fira ministan HKI Ehud Barack cewa ya yi; rashin tsayyar manufa ta gwmanatin Netanyahu ne ya sa har yanzu Hamas din yake ci gaba da iko da Gaza. Ya kuma kara da cewa, ba ta hanyar kashe shugabannin Hamas ne za a kawo karshenta ba, sai dai ta hanyar samar da wadanda za su maye gurbinta.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa

Wani jami’in ɗan sanda, SP Mustapha Garba Gumau, ya yi gamo ajalinsa a wani hatsarin mota yayin da ya rage aƙalla sa’a ɗaya a ɗaura masa aure.

Aminiya ta ruwaito cewa, ajali ya katse hanzarin jami’in ne a kan hanyar Gumau zuwa Magaman-Gumau da ke Ƙaramar Hukumar Toro ta Jihar Bauchi, inda za a ɗaura masa aure.

Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina

SP Gumau wanda hatsarin ya rutsa da shi da abokansa ya rasu ne da misalin ƙarfe 9 yayin da ake shirin ɗaura masa aure da misalin ƙarfe 10 na safiyar ranar Asabar.

Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Bauchi, CSP Mohammed Ahmed Wakil ya fitar ta ce an tabbatar da rasuwar matashin da ke shirin angwancewa bayan an garzaya da shi asibiti.

Wakil ya ce jami’in ya rasu tare da wasu abokansa biyu da ke cikin wata mota ƙirar marsandi bayan sun yi karo da wata motar ƙirar Opel Vectra.

Sanarwar ta ambato Kwamishinan ’yan sandan Bauchi, CP Auwal Sani Omolori yana jajanta wa iyalan mamatan da kuma addu’ar mutuwa ta zamanto hutu a gare su.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Ba’a Rufe Kofar Diblomasiyya Ba, Matukar HKI Ta Dakatar Da Kaiwa Kasar HKI
  • Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila
  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran