Aminiya:
2025-08-01@06:55:17 GMT

’Yan bindiga sun kashe fasto a Gombe

Published: 10th, February 2025 GMT

’Yan bindiga sun kashe wani fasto, Rabaran Bala Galadima yayin harin da suka kai garin Lubo da ke Ƙaramar Hukumar Yamaltu Deba a Jihar Gombe.

Aminiya ta ruwaito cewa, ’yan bindigar sun kuma yi fashin kuɗi har Naira dubu 300 a yayin harin da suka kai cikin dare wayewar gari Lahadi.

Wani mazaunin garin ya bayyana cewa maharan, waɗanda sun kai takwas, sun kai farmakin ne da misalin karfe 1 zuwa 3 na dare, inda suka firgita jama’a da harbe-harbe kafin su kutsa cikin gidan wani mutum mai suna Musa Puma.

Majiyar ta ce maharan sun rutsa matar gidan da bindiga inda suka karbi kuɗi naira dubu dari 300 tare da yin garkuwa da ɗaya daga cikin ’ya’yansu da kuma barazanar kashe shi muddin aka yi musu tirjiya.

Shi kuwa Faston Cocin ECWA na garin Lubo, Rabaren Bala Galadima, ya rasa ransa ne bayan da maharan suka harbe shi a gadon baya a gidansa, lamarin da ya girgiza al’ummar garin.

Gwamnati Ta Yi Allah Wadai

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi Allah wadai da kisan Rabaren Bala Galadima, tare da bayyana alhininsa kan wannan aika-aika.

A wata sanarwa da Babban Daraktan Yada Labarai na Gwamnatin Jihar, Isma’illa Uba Misilli ya fitar a ranar Litinin, gwamnan ya bayyana kisan a matsayin zagon kasa ga zaman lafiya da tsaron Jihar Gombe.

“Wannan kisan Fasto Rabaren Bala Galadima babban abin takaici ne. Babu shakka, wannan aiki zagon ƙasa ne ga zaman lafiya da tsaro wanda Jihar Gombe ta shahara da shi.

“Ba za mu lamunci irin waɗannan abubuwa da ke kawo cikas ga zaman lafiya a jiharmu ba,” in ji Gwamna Yahaya.

Gwamnan ya kuma umurci hukumomin tsaro da su zakulo waɗanda suka aikata wannan ɗanyen aiki tare da gurfanar da su a gaban kotu.

Ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da goyon baya ga hukumomin tsaro domin tabbatar da cewa irin wannan lamari bai sake faruwa ba.

Gwamnati ta kuma yi kira ga al’ummar jihar da su kasance masu kula da tsaron kansu tare da sanar da hukumomin tsaro duk wani motsi da suke zargin zai iya kawo barazana ga zaman lafiya.

Gwamnan ya ba da tabbacin cewa ba za su yi ƙasa a gwiwa ba wajen ganin an kawo ƙarshen ayyukan ta’addanci a jihar.

A nasu ɓangaren, rundunar ’yan sandan Gombe ta bakin mai magana da yawunta, DSP Buhari Abdullahi ta ce tuni aka aike da jami’ai domin gudanar da bincike kuma nan gaba kaɗan za su fitar da jawabi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga jihar Gombe mahara ga zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Dangane da tattaunawar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka da aka gudanar a kwanan nan, Guo Jiakun ya bayyana cewa, ana fatan bangaren Amurka zai yi aiki tare da Sin wajen amfani da tsarin tattaunawa kan tattalin arziki da cinikayya tsakanin kasashen biyu, don sa kaimi ga bunkasa dangantakar dake tsakanin Sin da Amurka cikin kwanciyar hankali.

Dangane da batun Falasdinu kuwa, Guo Jiakun ya ce, “manufar kafa kasashe biyu” ita ce hanya daya tilo ta hakika ta warware matsalar Falasdinu, kuma kasar Sin tana goyon bayan al’ummar Falasdinu wajen kafa kasa mai cin gashin kanta.(Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki
  • Manyan makarantu 2 ne kacal ke da rajista a Katsina — Gwamnati
  • Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • ’Yan bindiga sun tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja
  • Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga
  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri