Aminiya:
2025-06-16@00:54:23 GMT

’Yan bindiga sun kashe fasto a Gombe

Published: 10th, February 2025 GMT

’Yan bindiga sun kashe wani fasto, Rabaran Bala Galadima yayin harin da suka kai garin Lubo da ke Ƙaramar Hukumar Yamaltu Deba a Jihar Gombe.

Aminiya ta ruwaito cewa, ’yan bindigar sun kuma yi fashin kuɗi har Naira dubu 300 a yayin harin da suka kai cikin dare wayewar gari Lahadi.

Wani mazaunin garin ya bayyana cewa maharan, waɗanda sun kai takwas, sun kai farmakin ne da misalin karfe 1 zuwa 3 na dare, inda suka firgita jama’a da harbe-harbe kafin su kutsa cikin gidan wani mutum mai suna Musa Puma.

Majiyar ta ce maharan sun rutsa matar gidan da bindiga inda suka karbi kuɗi naira dubu dari 300 tare da yin garkuwa da ɗaya daga cikin ’ya’yansu da kuma barazanar kashe shi muddin aka yi musu tirjiya.

Shi kuwa Faston Cocin ECWA na garin Lubo, Rabaren Bala Galadima, ya rasa ransa ne bayan da maharan suka harbe shi a gadon baya a gidansa, lamarin da ya girgiza al’ummar garin.

Gwamnati Ta Yi Allah Wadai

Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya, ya yi Allah wadai da kisan Rabaren Bala Galadima, tare da bayyana alhininsa kan wannan aika-aika.

A wata sanarwa da Babban Daraktan Yada Labarai na Gwamnatin Jihar, Isma’illa Uba Misilli ya fitar a ranar Litinin, gwamnan ya bayyana kisan a matsayin zagon kasa ga zaman lafiya da tsaron Jihar Gombe.

“Wannan kisan Fasto Rabaren Bala Galadima babban abin takaici ne. Babu shakka, wannan aiki zagon ƙasa ne ga zaman lafiya da tsaro wanda Jihar Gombe ta shahara da shi.

“Ba za mu lamunci irin waɗannan abubuwa da ke kawo cikas ga zaman lafiya a jiharmu ba,” in ji Gwamna Yahaya.

Gwamnan ya kuma umurci hukumomin tsaro da su zakulo waɗanda suka aikata wannan ɗanyen aiki tare da gurfanar da su a gaban kotu.

Ya yi kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da goyon baya ga hukumomin tsaro domin tabbatar da cewa irin wannan lamari bai sake faruwa ba.

Gwamnati ta kuma yi kira ga al’ummar jihar da su kasance masu kula da tsaron kansu tare da sanar da hukumomin tsaro duk wani motsi da suke zargin zai iya kawo barazana ga zaman lafiya.

Gwamnan ya ba da tabbacin cewa ba za su yi ƙasa a gwiwa ba wajen ganin an kawo ƙarshen ayyukan ta’addanci a jihar.

A nasu ɓangaren, rundunar ’yan sandan Gombe ta bakin mai magana da yawunta, DSP Buhari Abdullahi ta ce tuni aka aike da jami’ai domin gudanar da bincike kuma nan gaba kaɗan za su fitar da jawabi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga jihar Gombe mahara ga zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu

Hukumomin ’yan sandan Najeriya tare da haɗin gwiwar wasu hukumomin tsaro sun samu gagarumar nasara a ƙoƙarin da suke na daƙile munanan laifuka a ƙasar.

Na baya-bayan nan dai shi ne ceto mutanen da aka sace, da kashe wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da kuma ƙwato manyan bindigogi da alburusai a jihohin Delta da Katsina.

Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan, Olumuyiwa Adejobi ya fitar, ya ce a jihar Katsina an samu gagarumar nasara a ranar 8 ga watan Yunin 2025, inda haɗin gwiwar JTF da suka haɗa da jami’an ’yan sanda da sauran jami’an tsaro suka daƙile wani yunƙurin yin garkuwa da mutane a hanyar ƙauyen Danmusa  zuwa  Mara Dangeza a ƙaramar hukumar Danmusa.

Adejobi ya ce hakan na iya yiwuwa ne ta hanyar shigar da wasu gungun ’yan bindiga da suka yi yunƙurin guduwa da waɗanda aka yi garkuwa da su a wani artabu da ya kai ga ceto mutum 11.

Nasarar da aka samu yankin Kudu maso Kudu

A halin da ake ciki kuma, a yankin Kudu maso Kudu, Jihar Delta, hukumar ’yan sanda ta kama wani Abubakar Hassan, wanda babban wanda ake zargi da aikata laifin satar mutane ne a tsakanin jihohin Delta da Ribas da Imo, da Enugu.

Jami’an da ke da alaƙa da samun nasarar sun yi hakan ne yayin da suke aiki da sahihan bayanai.

A yayin da ake yi masa tambayoyi, Hassan ya bayyana cewa shi ne ya jagoranci gudanar da hari a yankin Ughelli-Ozoro na jihar mai arzikin man fetur.

Ya kuma jagoranci jami’an ’yan sanda zuwa maɓoyarsa a wani daji da ke Ozoro. A can jami’an sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu da tarin alburusai huɗu da harsashi guda talatin da biyu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Hajjin 2025: Yadda Alhazan Nijeriya 7 Suka Rasa Rayukansu A Saudi Arabiya