Aminiya:
2025-06-15@13:43:09 GMT

’Yan gida daya sun yi wa ma’aurata dukan kawo wuka a Kano

Published: 10th, February 2025 GMT

An gurfanar da wasu mutum uku ’yan uwan juna kan yi wa wata matar aure da mijinta dukan kawo wuƙa a yankin Karamar Hukumar Gezawa da ke Jihar Kano.

An gurfanar da su ne a gaban Babbar Kotun Musulunci ta Gazawa kan zargin yi wa matar auren karaya uku a ƙafarta da hannunta bayan sun yi mata dukan kawo wuƙa tare da ji mata raunuka.

Sun kuma ƙuƙƙuje mijinta da ya yi ƙoƙarin ceton ta bayan shi ma suka lakaɗa masa duka.

Ana tuhumar su laifin yin kutse da yin barazana da haɗa kai wajen aikata laifi da ji wa mutane munanan raunuka.

’Yan sanda sun ba al’ummar Sheka awa 24 su kawo sunayen ’yan daba Ɗan fashi ya yi wa ɗaliban jami’a uku fyaɗe

Duk waɗanda ake zargin sun amsa laifukan da ake tuhumar su da aikatawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dukan kawo wuka

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran

Iran ta sanar da soke zaman tattaunawa da ya kamata ta yi da Amurka kan batun nikiliyarta a Oman yau Lahadi saka makon hare-haren da Isra’ila ta kai mata a ranar Juma’a.

Bayanai sun ce a wannan Lahadin ce ya kamata a gudanar da ganawa ta shida tsakanin wakilan Amurka da na Iran a birnin Musqat na Oman.

Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe

Sai dai kakakin Ministan harkokin wajen Iran, Esmaeil Baqaei ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, Amurka ta nuna fuska biyu, inda a gefe guda take tattaunawar cimma masalahar jingine ƙera nukiliya da Iran, amma a ɗaya gefen kuma ta goyi bayan harin da Isra’ila ta kai mata.

Iran ta zargi Amurka da goyon bayan harin da Isra’ila ta kai mata, sannan kuma ta ce tattaunawar yarjejeniyar dakatar da ƙera makamin ƙare dangi na nukiliya da take yi da Amurkar ba ta da wani amfani.

A nasa ɓangaren, Ministan harakokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya ce babu buƙatar ci gaba da tattaunawa da aka faro tsakiyar watan Afirilun wannan shekara lura da harin dabbanci da Isra’ila ta kai mata.

Kafofin yaɗa labarai da dama a Iran sun shaida cewa guda daga cikin masu baiwa jagoran addinin musluncin Iran ayatoAllah Ali Khamenei kuma mai taka muhimmiyar rawa a tattaunawar, Ali Shamkhani, na daga cikin waɗanda su ka ji rauni a hare-haren na Isra’ila.

Tun farko Isra’ila ce ta fara kai wa Iran hari kan cibiyoyin nukiliyarta tare da halaka manyan hafsoshin tsaronta, cikin daren Alhamis zuwa wayewar garin Juma’a, kuma ta ci gaba da kai farmaki da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa, mafarin buɗe kofar wani sabon rikici a tsakanin ƙasashen biyu da suka jima suna adawa da juna tsawon shekaru.

Harin ramuwar gayya da Iran ta kai wa Isra’ila da safiyar Asabar ya halaka mutane uku, tare da jikkata wasu da dama a biranen Jerusalem da Tel Aviv, inda hukumomin Isra’ila ke ci gaba da gargaɗin ‘yan kasar su nemi mafaka.

A wani jawabi da jagoran addini na Iran Ayatollah Ali Khamenei ya gabatarwa al’ummar kasar ranar Juma’a, ya ce ba za su saurara wa Isra’ila ba sakamakon munin abin da ta aikata musu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da muka soke tattaunawar nukiliya da Amurka — Iran
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
  • ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2