HausaTv:
2025-06-15@19:41:07 GMT

Iran Ce Kasa Ta 10 A Duniya Wajen Samar Da Wutar Lantarki

Published: 9th, February 2025 GMT

An bayyana cewa  Iran ce kasar ta 10 a duniya wajen samar da wutar lantarki, da yawan megawati dubu 94 da 846.

Manajan da yake kula da tsara manyan ayyuka a ma’aikatar makamashi ta Iran, Behruz Muradi ya bayyana cewa, shekru 46 da su ka gabata, wato a lokacin juyin juya halin musulunci, yawan megawatin da Iran take samarwa ya yi kasa da wanda ake da shi a yanzu har sau hudu.

Manajan ya kuma kara da cewa wutar lantarki da ake da ita a Iran da karfin tsarin da take da shi, tana taka rawa mai muhimmanci wajen gina tattalin arzikin kasar. Haka nan kuma ya ce, da akwai kyakkyawan tsarin da ake da shi ya samar da cigaba a cikin bangarorin ruwan sha, da kuma noma da kiwo.

Behruz Muradi ya kuma ce, ci gaban da aka samu a fagen wutar lantarki a Iran yana daga cikin nasararon juyin juya halin musulunci.

Hanyoyin da Iran take samar da wutar lantarki, sun hada da madatsun ruwa, iska, hasken rana da kuma wasu sabbin hanyoyin na zamani.

Dangane da yawan garuruwan da suke da wutar lantarki a Iran, manaja Muradi ya ce, A halin yanzu da akwai kauyuka da sun kai 58,000, da 829 da suke da wutar lantarki.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: da wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Yarima Mai Jiran Gadon Saudiyya Ya Jaddada Goyon Bayan Kasarsa Ga Iran

Yarima mai jiran gadon Saudiyya ya tabbatarwa shugaban kasar Iran cewa: Saudiyya tana goyon bayan Iran

Yariman mai jiran gadon Saudiyya Mohammed bin Salman ya tabbatar da hakan ne a wata tattaunawa ta wayar tarho da shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian a yammacin jiya Asabar, yana mai jaddada cewa: Masarautar Saudiyya da daukacin al’ummar musulmin duniya sun hadu a kan goyon bayan Iran.

Yarima mai jiran gadon sarautar Saudiyya ya ce: Dukkanin al’ummomin kasashen musulmi a yau suna da hadin kai da jaddada goyon bayansu ga Iran, kuma yana iyaka kokarinsa a fagen diflomasiyya da matsin lamba na kasa da kasa don dakatar da wuce gona da irin da ‘yan sahayoniyya suke yi kan Iran.

Bin Salman ya yi Allah wadai da hare-haren rashin adalci da ‘yan sahayoniyya suke kaiwa Iran.

Ya kuma bayyana jimaminsa tare da jajantawa al’ummar kasar Iran dangane da wadannan hare-hare da suka rutsa da su, yana mai jaddada cewa: Saudiyya tana da tabbataccen matsayi kan tsayawa tare da ‘yar uwarta Jamhuriyar Musulunci ta Iran, kuma duniyar musulmi a yau ta hade kan muryar daya wajen goyon bayan Iran.

Ya ci gaba da cewa: “Mun yi imanin cewa, gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila na neman ta hanyar kara kunna wutar rikici ta janyo Amurka a cikin tsakiyar rikici, amma suna da yakinin cewa martanin Iran a kan ma’aunin daidaito da matakan hankali zai dakile wannan  yunƙurin makirci.”

Bin Salman ya kuma jaddada cewa: Kasarsa ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen bayar da duk wani tallafi da ya dace ga ‘yan uwanta Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wang Yi Ya Tattauna Ta Wayar Tarho Da Ministocin Harkokin Wajen Iran Da Isra’ila
  • Yarima Mai Jiran Gadon Saudiyya Ya Jaddada Goyon Bayan Kasarsa Ga Iran
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Wutar Lantarki Mai Ƙarfi Ta Yi Ajalin Mutum Biyar A Gombe
  • Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Dukufa Wajen Karya Farashin Kayan Abinci – Minista
  • Bukatar Kara Yawan Masu Fitowa Kada Kuri’a A Zabuka Nan Gaba
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje