HausaTv:
2025-08-01@23:23:40 GMT

Iran Ce Kasa Ta 10 A Duniya Wajen Samar Da Wutar Lantarki

Published: 9th, February 2025 GMT

An bayyana cewa  Iran ce kasar ta 10 a duniya wajen samar da wutar lantarki, da yawan megawati dubu 94 da 846.

Manajan da yake kula da tsara manyan ayyuka a ma’aikatar makamashi ta Iran, Behruz Muradi ya bayyana cewa, shekru 46 da su ka gabata, wato a lokacin juyin juya halin musulunci, yawan megawatin da Iran take samarwa ya yi kasa da wanda ake da shi a yanzu har sau hudu.

Manajan ya kuma kara da cewa wutar lantarki da ake da ita a Iran da karfin tsarin da take da shi, tana taka rawa mai muhimmanci wajen gina tattalin arzikin kasar. Haka nan kuma ya ce, da akwai kyakkyawan tsarin da ake da shi ya samar da cigaba a cikin bangarorin ruwan sha, da kuma noma da kiwo.

Behruz Muradi ya kuma ce, ci gaban da aka samu a fagen wutar lantarki a Iran yana daga cikin nasararon juyin juya halin musulunci.

Hanyoyin da Iran take samar da wutar lantarki, sun hada da madatsun ruwa, iska, hasken rana da kuma wasu sabbin hanyoyin na zamani.

Dangane da yawan garuruwan da suke da wutar lantarki a Iran, manaja Muradi ya ce, A halin yanzu da akwai kauyuka da sun kai 58,000, da 829 da suke da wutar lantarki.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: da wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Za a fara yi wa ɗaliban jami’o’i gwajin ƙwaya — Gwamnatin Nijeriya

Gwamnatin Nijeriya ta bayanna cewa za ta soma yi wa ɗaliban jami’o’in ƙasar nan gwajin miyagun ƙwayoyi a wani mataki na daƙile yaɗuwar ta’ammali da ƙwayoyin.

Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya NAN ya ruwaito cewa, Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya tare da haɗin gwiwar Hukumar Yaƙi da Fataucin Miyagun Kwayoyi NDLEA ne za su jagoranci aikin.

Sarkin Gudi na Jihar Yobe, Isa Bunuwo Ibn Khaji ya rasu Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani

Hakan na zuwa ne bayan ganawar Shugaban Hukumar NDLEA, Birgediya Janar Buba Marwa mai ritaya da kuma ministan ilimin ƙasar, Olatunji Alausa a jiya Laraba.

Ɓangarorin biyu sun kuma amince da ɓullo da daftarin koyar da darasin ilimin ta’ammali da ƙwayoyi a makarantun sakandiren ƙasar.

Buba Marwa wanda ya jagoranci tawagar jagororin hukumar NDLEA ya bayyana cewa gwajin ƙwayar zai shafi duk ɗaliban jami’o’in da sabbin da za su shiga.

Yayin da yake jawabi a wajen ganawar, Buba Marwa ya ce za su mayar da hankali ne kan makarantun ƙasar, waɗanda ya ce akwai miliyoyin yara da ke ƙarƙashin kulawar ma’aikatar ilimin ƙasar.

Buba Marwa ya ce rashin daƙile ta’ammali da miyagun ƙwayoyi daga wajen ƙananan yara ya taimaka wajen jefa matasan ƙasar cikin ayyukan ta’addanci da fashin daji da sauran miyagun laifuka.

Ya bayyana mummunan tasirin shan miyagun ƙwayoyi a kan matasan ƙasar, yana mai cewa yaƙi da miyagun ƙwayoyi yaki ne don ceton rayukan matasan Nijeriya.

Marwa ya ce a yanzu hankalin hukumar zai fi karkata ne zuwa makarantu da cibiyoyin ilimi, yana mai ƙarawa da cewa akwai miliyoyin yaran Nijeriya da ke ƙarƙashin kulawar ma’aikatar ilimi, kuma wannan abu ne mai matuƙar muhimmanci.

Shugaban hukumar ta NDLEAn ya ce a dalilin goyon bayan da suka samu karkashin Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu a tsawon shekaru biyu da suka gabata, hukumar ta kama mutane 40,887 da ake zargi da aikata laifuka, ta daure 8,682, kuma ta kwace tan 5,507 na miyagun ƙwayoyi.

A cewarsa, tun daga watan Janairu bara, an ƙwace ƙwayar tramadol da ta wuce ƙwaya biliyan ɗaya, wanda kudinta ya fi naira tiriliyan ɗaya.

Shugaban NDLEA ya jaddada cewa Shugaba Tinubu yana kuma tallafa wa hukumar wajen gina cibiyoyi bakwai na gyaran masu fama da shan miyagun ƙwayoyi, baya ga sauran cibiyoyi 30 da ke karkashin umarnin NDLEA a faɗin ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
  • Bashin Naira Tiriliyan 4 Na Barazanar ɗorewar Wutar Lantarki A Nijeriya – Minista
  • Za a fara yi wa ɗaliban jami’o’i gwajin ƙwaya — Gwamnatin Nijeriya
  • Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres
  • An Yaba Da Kwazon Shugaba Bola Ahmad Tinubu
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata
  • Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila
  • Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa
  • Gwamnatin Jihar Kano Ta Kaddamar da Manufar Sauyin Yanayi